Tsallake zuwa abun ciki

Ayoyin Littafi Mai Tsarki game da Prayer

720 ayoyi · 120 fannoni

Mahimman ayoyin Littafi Mai Tsarki

Tace bisa littafi
  1. gama ya farfashe ƙofofin tagulla ya kuma ragargaza ƙyamaren ƙarfe.

  2. Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa suka kuwa sha wahala saboda laifofinsu.

  3. Ba su so su ga abinci ba suka kuwa kai bakin mutuwa.

  4. Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.

  5. Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su ya kuɓutar da su daga kabari.

  6. Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.

  7. Sa’ad da aka yi masa shari’a, bari a same shi da laifi, bari kuma addu’o’insa su hukunta shi.

  8. Bari ’ya’yansa su zama marayu matarsa kuma gwauruwa.

  9. Bari ’ya’yansa su zama masu yawo suna bara; bari a yi ta koransu daga gidajensu da suke kufai.

  10. Bari mai binsa bashi yă ƙwace dukan abin da yake da shi; bari baƙi su washe amfanin aikinsa.

  11. Bari kada kowa yă yi masa alheri ko yă ji tausayin marayunsa.

  12. Bari duk zuriyarsa su mutu, a shafe sunayensu daga tsara mai zuwa.

  13. Bari a tuna da laifin kakanninsa a gaban Ubangiji; bari kada a taɓa shafe zunubin mahaifiyarsa.

  14. Bari zunubansu su kasance a gaban Ubangiji kullum, don yă sa a manta da su daga duniya.

  15. Gama bai taɓa yin tunanin yin alheri ba, amma ya tsananta wa matalauta da mabukata da kuma masu fid da zuciya har suka mutu.

  16. Yana jin daɗin la’antarwa, bari yă dawo a kansa; ba ya son sa albarka, bari kada kowa yă sa masa albarka.

  17. Ya sa la’antarwa kamar rigarsa; ta shiga cikin jikinsa kamar ruwa, cikin ƙasusuwansa kamar mai.

  18. Bari tă zama kamar mayafin da aka ɗaura kewaye da shi, kamar ɗamara da aka ɗaura kewaye da shi har abada.

  19. Bari wannan yă zama sakayyar Ubangiji ga masu zargina, ga waɗanda suke mugayen maganganu a kaina.

  20. Amma kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi da ni da kyau saboda sunanka; ta alherin ƙaunarka, ka cece ni.

  21. Gama ni matalauci ne mai bukata kuma, zuciyata kuwa ta yi rauni a cikina.

  22. Na ɓace kamar inuwar yamma; ana kakkaɓe ni kamar fāra.

  23. Gwiwoyina suna mutuwa saboda azumi; jikina ya rame ba kuma ƙarfi.

  24. Na zama abin dariya ga masu zargina; sa’ad da suka gan ni, suka kaɗa kawunansu.

  25. Ka taimake ni, ya Ubangiji Allahna; ka cece ni bisa ga ƙaunarka.