Tsallake zuwa abun ciki

Ayoyin Littafi Mai Tsarki game da Prayer

720 ayoyi · 120 fannoni

Mahimman ayoyin Littafi Mai Tsarki

Tace bisa littafi
  1. Bari su san cewa hannunka ne, cewa kai ne, ya Ubangiji, ka yi shi.

  2. Za su iya la’anta, amma kai za ka sa albarka; sa’ad da suka tasar za su sha kunya, amma bawanka zai yi farin ciki.

  3. Masu zargina za su sha kunya za a rufe su da kunya kamar mayafi.

  4. ’Ya’yansa za su zama manya a ƙasar; tsaran masu aikata gaskiya za su sami albarka.

  5. Ba gare mu ba, ya Ubangiji, ba gare mu ba amma ga sunanka yă sami ɗaukaka, saboda ƙaunarka da amincinka.

  6. Me ya sa al’ummai suke cewa, “Ina Allahnsu?”

  7. Ina ƙaunar Ubangiji, gama ya ji muryata; ya ji kukata ta neman jinƙai.

  8. Domin ya juye kunnensa gare ni, zan kira gare shi muddin ina da rai.

  9. Sai na kira ga sunan Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji, ka cece ni!”

  10. Cikin azabata na yi kuka ga Ubangiji, ya kuwa amsa ta wurin ’yantar da ni.

  11. Zan yi maka godiya, domin ka amsa mini; ka zama mai cetona.

  12. Na ba da labari hanyoyina ka kuma amsa mini; ka koya mini ƙa’idodinka.

  13. Ka cika alkawarinka ga bawanka, saboda a ji tsoronka.

  14. sa’an nan zan amsa wa masu cin mutuncina, gama na dogara ga maganarka.

  15. Kada ka ƙwace maganarka daga bakina, gama na sa zuciyata a dokokinka.

  16. Tuna da maganarka ga bawanka, gama ka ba ni bege.

  17. Na nemi fuskarka da dukan zuciyata; ka yi mini alheri bisa ga alkawarinka.

  18. Hannuwanka ne suka yi suka kuma siffanta ni; ka ba ni ganewa don in koyi umarnanka.

  19. Bari masu girman kai su sha kunya saboda abubuwa marasa kyau da suke yi mini ba dalili; amma zan yi tunani a kan farillanka.

  20. Har yaushe bawanka zai yi ta jira? Yaushe za ka hukunta masu tsananta mini?

  21. Ka cece ni, gama ni naka ne; na yi ƙoƙarin neman farillanka.

  22. Ka raya ni bisa ga alkawarinka, zan kuwa rayu; kada ka bari a gwale sa zuciyata.

  23. Ka yi da bawanka bisa ga ƙaunarka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.

  24. Na yi kira da dukan zuciyata; ka amsa mini, ya Ubangiji, zan kuwa yi biyayya da ƙa’idodinka.

  25. Na yi kira gare ka; ka cece ni zan kuwa kiyaye farillanka.