Tsallake zuwa abun ciki

circa 1406–1380 BC

Conquest of Canaan

Joshua leads Israel across the Jordan into the promised land, defeating the Canaanite kingdoms one by one.

658 ayoyi · 1 littafi da aka rufe

Ayoyi daga wannan lokacin

  1. Yoshuwa 19:31kusan 1443 K.H.

    Garuruwan nan da ƙauyukansu su ne gādon da kabilar Asher ta samu bisa ga iyalansu.

  2. Yoshuwa 19:32kusan 1443 K.H.

    Ƙuri’a ta shida ta fāɗa a kan kabilar Naftali, bisa ga iyalansu.

  3. Yoshuwa 19:33kusan 1443 K.H.

    Iyakarsu ta kama daga Helef, daga babban itacen Mamre nan da yake a Za’anannim, ta wuce Adami Nekeb da Yabneyel zuwa Lakkum, ta kuma ƙarasa a Urdun.

  4. Yoshuwa 19:34kusan 1443 K.H.

    Iyakar kuma ta juya yamma ta cikin Aznot-Tabo ta ɓulla a Hukkok. Ta taɓa Zebulun a kudu, Asher a yamma, da kuma Urdun a gabas.

  5. Yoshuwa 19:35kusan 1443 K.H.

    Biranen da suke da katanga su ne Ziddim, Zer, Hammat, Rakkat, Kinneret,

  6. Yoshuwa 19:36kusan 1443 K.H.

    Adama, Rama, Hazor,

  7. Yoshuwa 19:37kusan 1443 K.H.

    Kedesh, Edireyi, En Hazor,

  8. Yoshuwa 19:38kusan 1443 K.H.

    Yiron, Migdal El, Horem, Bet-Anat da Bet-Shemesh. Garuruwa goma sha tara ke nan da ƙauyukansu.

  9. Yoshuwa 19:39kusan 1443 K.H.

    Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne rabon da kabilar Naftali ta samu, bisa ga iyalansu.

  10. Yoshuwa 19:40kusan 1443 K.H.

    Ƙuri’a ta bakwai ta fāɗa a kan kabilar Dan, bisa ga iyalansu.

  11. Yoshuwa 19:41kusan 1443 K.H.

    Ƙasarsu ta gādo ta haɗa da, Zora, Eshtawol, Ir Shemesh,

  12. Yoshuwa 19:42kusan 1443 K.H.

    Shalim, Aiyalon, Itla,

  13. Yoshuwa 19:43kusan 1443 K.H.

    Elon, Timna, Ekron,

  14. Yoshuwa 19:44kusan 1443 K.H.

    Elteke, Gibbeton, Ba’alat,

  15. Yoshuwa 19:45kusan 1443 K.H.

    Yehud, Bene-Berak, Gat-Rimmon,

  16. Yoshuwa 19:46kusan 1443 K.H.

    Me Yarkon da Rakkon tare da sashen da yake fuskantar Yaffa.

  17. Yoshuwa 19:47kusan 1443 K.H.

    (Amma ya zama wa mutanen kabilar Dan da wahala su mallaki ƙasar da aka ba su gādo, saboda haka sai suka nufi Leshem suka ci su da yaƙi, suka karkashe mutanen wurin, suka mallake ta, suka zauna a ciki. Suka kuma sa wa Leshem, sunan kakansu, wato, Dan.)

  18. Yoshuwa 19:48kusan 1443 K.H.

    Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne gādon kabilar Dan, bisa ga iyalansu.

  19. Yoshuwa 19:49kusan 1443 K.H.

    Sa’ad da aka gama raba gādon ƙasar bisa ga ƙuri’a. Sai Isra’ilawa suka ba Yoshuwa ɗan Nun nasa rabo a cikinsu,

  20. Yoshuwa 19:50kusan 1443 K.H.

    yadda Ubangiji ya umarta, suka ba shi garin da ya ce a ba shi, Timnat Serad a ƙasar tudu ta Efraim. Ya kuma gina garin ya zauna a can.

  21. Yoshuwa 19:51kusan 1443 K.H.

    Waɗannan su ne rabe-raben gādon da Eleyazar firist, Yoshuwa ɗan Nun, da kuma shugabannin kabilan iyalan Isra’ila suka rarraba ta hanyar jefa ƙuri’a a Shilo a gaban Ubangiji a ƙofar Tentin Sujada. Da haka suka yi suka gama rarraba ƙasar.

  22. Yoshuwa 20:1kusan 1443 K.H.

    Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa,

  23. Yoshuwa 20:2kusan 1443 K.H.

    “Ka gaya wa Isra’ilawa su keɓe waɗansu birane su zama biranen mafaka kamar yadda na umarce ku ta wurin Musa,

  24. Yoshuwa 20:3kusan 1443 K.H.

    domin idan wani ya kashe wani bisa kuskure ba da niyyar yin kisankai ba, mutumin zai iya gudu zuwa can yă fake don kada a kashe shi.

  25. Yoshuwa 20:4kusan 1443 K.H.

    Lokacin da ya gudu zuwa ɗaya daga cikin biranen nan, sai yă tsaya a ƙofar birnin yă gaya wa dattawan wannan birni damuwarsa. Sa’an nan su karɓe shi su ba shi wurin zama a cikin birninsu.