- English
- King James KJV
- Complete Jewish CJB
- World English WEBM
- Berean Standard BSB
- American Standard ASV
- Geneva GNV
- Young's Literal YLT
- Douay-Rheims DRC
- International
- Shqip ALB
- العربية SVD
- বাংলা BN-IRV
- မြန်မာ Judson
- 简体文 CUV-S
- 繁體中文 CUV-T
- Čeština BKR
- Nederlands STVE
- Français LSG
- Deutsch SCH
- Ελληνικά Vamvas
- ગુજરાતી GU-IRV
- Hausa HCB
- עברית Hebrew
- हिन्दी HCV
- Magyar KAROLI
- Bahasa Indonesia INDO-TB
- Italiano Diodati
- 日本語 Kougo
- 한국어 Korean
- മലയാളം MAL
- मराठी MRCV
- Norsk DNB
- فارسی OPV
- Polski BG
- Português Almeida
- Română Cornilescu
- Русский Synodal
- Español RVG
- Kiswahili Neno
- Svenska SV1917
- Tagalog TAG-ADB
- தமிழ் TCV
- తెలుగు TSA
- ภาษาไทย THAI-KJV
- Українська Ohienko
- Tiếng Việt CADMAN
- Yorùbá YCB
Ayoyin Littafi Mai Tsarki game da Pride
Mahimman ayoyin Littafi Mai Tsarki
Sa’ad da Haman ya ga cewa Mordekai ba ya durƙusa ko yă girmama shi, sai ya fusata.
Amma daƙiƙin mutum ba ya taɓa zama mai hikima kamar dai a ce ba a taɓa haihuwar ɗan aholaki horarre.
“Ba shakka ku ne mutanen nan, hikima za tă mutu tare da ku!
Amma ni ma ina da hankali kamar ku; ba ku fi ni ba. Wane ne bai san duk waɗannan abubuwan ba?
Abin da kuka sani, ni ma na sani; ba ku fi ni ba.
In da za ku yi shiru gaba ɗaya! Zai zama muku hikima.
Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
“Mutum mai hikima zai amsa da surutai marasa kan gado ko yă cika cikinsa da iskar gabas?
Ko zai yi gardama da maganganun wofi maganganu marasa amfani?
Amma ka ma rena Allah ka hana a yi addu’a gare shi.
Zunubanka ne suke gaya maka abin da za ka ce; kana magana kamar mai wayo.
Bakinka zai kai ka yă baro, ba nawa ba; maganar bakinka za tă juya a kanka.
“Kai ne mutum na farko da aka fara haihuwa? Ko kai ne aka fara halitta kafin tuddai?
Kana sauraron shawarar Allah? Ko kana gani kai kaɗai ne mai hikima?
Me ka sani da ba mu sani ba? Wane fahimi kake da shi da ba mu da shi?
Masu furfura da tsofaffi suna gefenmu mutanen da sun girme babanka.
Ta’aziyyar Allah ba tă ishe ka ba. Maganarsa mai laushi ba tă ishe ka ba?
Don me ka bar zuciyarka ta kwashe ka, kuma don me idanunka suke haske,
har kake fushi da Allah kake kuma faɗar waɗannan maganganu daga bakinka?
Don me muke kamar shanu a wurinka, ka ɗauke mu mutanen wofi?
Kai da ka yayyage kanka don haushi, za a yashe duniya saboda kai ne? Ko kuma duwatsu za su matsa daga wurinsu?
Wane ne yake gaya masa abin da ya yi? Wane ne yake rama abin da ya yi?
Za a bizne shi a kabari, a kuma yi tsaron kabarinsa.
Ba tsofaffi ne kaɗai suke da hikima ba, ba masu yawan shekaru ne suke gane abin da yake daidai ba.
“Saboda haka nake ce muku, ku saurare ni; ni ma zan gaya muku abin da na sani.