Skip to content

Ayoyin Littafi Mai Tsarki game da Sin

210 ayoyi · 120 fannoni

Mahimman ayoyin Littafi Mai Tsarki

Tace bisa littafi
  1. Suna ce, “Ubangiji ba ya gani; Allah na Yaƙub bai kula ba.”

  2. Bari masu ƙaunar Ubangiji su ƙi mugunta, gama yana tsaron rayukan amintattunsa yana kuma kuɓutar da su daga hannun mugaye.

  3. Na ɓoye maganarka a cikin zuciyata don kada in yi maka zunubi.

  4. Ka bincike ni, ya Allah ka kuma san zuciyata; ka gwada ni ka kuma san damuwata.

  5. Duba ko akwai wani laifi a cikina, ka bishe ni a madawwamiyar hanya.

  6. Ɗana, in masu zunubi sun jarabce ka, kada ka yarda.

  7. In suka ce, “Zo mu tafi; mu yi kwanton ɓauna, mu nemi wani mu kashe, mu fāɗa wa marasa laifi;

  8. mu haɗiye su da rai gaba ɗaya kamar kabari, kamar waɗanda suke gangarawa zuwa rami;

  9. za mu sami dukiya masu daraja iri-iri, mu kuma cika gidajenmu da ganima;

  10. ka haɗa kai da mu, za mu kuwa raba abin da muka sato”

  11. Akwai abubuwa shida da Ubangiji ya ƙi, abubuwa bakwai da suke abin ƙyama gare shi,

  12. duban reni, harshe mai ƙarya, hannuwa masu zub da jinin marar laifi,

  13. zuciyar da take ƙulla mugayen dabaru, ƙafafun da suke sauri zuwa aikata mugunta,

  14. mai shaidar ƙarya wanda yake zuba ƙarairayi, da kuma mutumin da yake tā-da-na-zaune-tsaye a cikin ’yan’uwa.

  15. Jin tsoron Ubangiji shi ne ƙin mugunta; ina ƙin girman kai da fariya, halin mugunta da kuma muguwar magana.

  16. Hakkin adalai kan kawo musu rai, amma albashin mugaye kan kawo musu hukunci.

  17. Wawaye kan yi ba’a a gyaran zunubi, amma fatan alheri yana samuwa a cikin masu aikata gaskiya.

  18. Adalci yakan ɗaukaka al’umma, amma zunubi kan kawo kunya ga kowane mutane.

  19. Ubangiji yana ƙin hanyar mugaye amma yana ƙaunar waɗanda suke neman adalci.

  20. Ta wurin ƙauna da aminci akan yi kafarar zunubi; ta wurin tsoron Ubangiji mutum kan guji mugunta.

  21. Wa zai iya cewa, “Na kiyaye zuciyata da tsarki; ni mai tsabta ne marar zunubi kuma”?

  22. Girmankai da fariya, su ne fitilar mugaye, wannan kuwa zunubi ne!

  23. Makircin wawa zunubi ne, mutane kuma sukan yi ƙyamar mai ba’a.

  24. Duk wanda ya ɓoye zunubansa ba ya taɓa cin nasara, amma duk wanda ya furta ya kuma ƙi su yakan sami jinƙai.

  25. waɗanda sukan ɗauka su tsarkaka ne a ganinsu alhali kuwa ƙazamai ne su;