- English
- King James KJV
- Complete Jewish CJB
- World English WEBM
- Berean Standard BSB
- American Standard ASV
- Geneva GNV
- Young's Literal YLT
- Douay-Rheims DRC
- International
- Shqip ALB
- العربية SVD
- বাংলা BN-IRV
- မြန်မာ Judson
- 简体文 CUV-S
- 繁體中文 CUV-T
- Čeština BKR
- Nederlands STVE
- Français LSG
- Deutsch SCH
- Ελληνικά Vamvas
- ગુજરાતી GU-IRV
- Hausa HCB
- עברית Hebrew
- हिन्दी HCV
- Magyar KAROLI
- Bahasa Indonesia INDO-TB
- Italiano Diodati
- 日本語 Kougo
- 한국어 Korean
- മലയാളം MAL
- मराठी MRCV
- Norsk DNB
- فارسی OPV
- Polski BG
- Português Almeida
- Română Cornilescu
- Русский Synodal
- Español RVG
- Kiswahili Neno
- Svenska SV1917
- Tagalog TAG-ADB
- தமிழ் TCV
- తెలుగు TSA
- ภาษาไทย THAI-KJV
- Українська Ohienko
- Tiếng Việt CADMAN
- Yorùbá YCB
circa AD 48–96
Letters to the Churches
Paul and other apostles write to strengthen, correct, and encourage the scattered churches across the Roman world.
Ayoyi daga wannan lokacin
- 1 Korintiyawa 16:5kusan 59 M.
Bayan na zazzaga Makidoniya, zan zo wurinku, domin zan ratsa ta Makidoniya.
- 1 Korintiyawa 16:6kusan 59 M.
Wataƙila zan ɗan jima a wajenku, ko ma in ci damina a can, domin ku yi mini rakiya a tafiyata, duk inda za ni.
- 1 Korintiyawa 16:7kusan 59 M.
Ba na so in gan ku yanzu in wuce kawai, ina fata zan yi ’yan kwanaki tare da ku, in Ubangiji ya yarda.
- 1 Korintiyawa 16:8kusan 59 M.
Sai dai zan kasance a Afisa har lokacin Fentekos,
- 1 Korintiyawa 16:9kusan 59 M.
domin an buɗe mini wata hanya mai fāɗi don aiki mai amfani, ko da yake akwai mutane da yawa masu gāba da ni.
- 1 Korintiyawa 16:10kusan 59 M.
In Timoti ya zo, ku tabbata ya sami sakewa a cikinku, domin aikin Ubangiji yake yi kamar yadda nake yi.
- 1 Korintiyawa 16:11kusan 59 M.
Kada fa wani yă ƙi karɓansa. Ku sallame shi lafiya, domin yă koma wurina. Ina duban hanyarsa tare da ’yan’uwa.
- 1 Korintiyawa 16:12kusan 59 M.
Batun ɗan’uwanmu Afollos kuwa, na roƙe shi sosai yă zo wurinku tare da ’yan’uwa. Bai so zuwa yanzu ba, amma zai zo in ya sami zarafi.
- 1 Korintiyawa 16:13kusan 59 M.
Ku zauna a faɗake; ku dāge cikin bangaskiya; ku zauna da ƙarfafawa; ku yi ƙarfi.
- 1 Korintiyawa 16:14kusan 59 M.
Ku yi kome da ƙauna.
- 1 Korintiyawa 16:15kusan 59 M.
Kun san cewa iyalin gidan Istifanas ne suka fara tuba a Akayya. Sun kuma ba da kansu ga yi wa tsarkaka hidima. Ina roƙonku ’yan’uwa,
- 1 Korintiyawa 16:16kusan 59 M.
ku ba da kanku ga irin waɗannan, ga kuma kowa da ya haɗa hannu a aikin, yana kuma faman a cikinsa.
- 1 Korintiyawa 16:17kusan 59 M.
Na yi farin ciki da isowar Istifanas, Fortunatus da Akaikus, domin sun biya bukatar da ba ku iya biya ba.
- 1 Korintiyawa 16:18kusan 59 M.
Gama sun wartsake ruhuna da kuma naku. Ya kamata ku girmama irin waɗannan mutane.
- 1 Korintiyawa 16:19kusan 59 M.
Ikkilisiyoyin da suke a lardin Asiya suna gaisuwa. Akwila da Firiskila suna gaishe ku sosai cikin Ubangiji, haka ma ikkilisiyar da takan taru a gidansu.
- 1 Korintiyawa 16:20kusan 59 M.
Dukan ’yan’uwa a nan suna gaisuwa. Ku gai da juna da sumba mai tsarki.
- 1 Korintiyawa 16:21kusan 59 M.
Ni, Bulus nake rubuta wannan gaisuwa da hannuna.
- 1 Korintiyawa 16:22kusan 59 M.
Duk wanda ba ya ƙaunar Ubangiji, la’ana ta zauna a kansa. Zo, ya Ubangiji!
- 1 Korintiyawa 16:23kusan 59 M.
Alherin Ubangiji Yesu yă kasance tare da ku.
- 1 Korintiyawa 16:24kusan 59 M.
Ina gaishe ku duka, gaisuwar ƙaunata cikin Kiristi Yesu. Amin.
- 2 Korintiyawa 1:1kusan 60 M.
Bulus, manzon Kiristi Yesu ta wurin nufin Allah, da kuma daga Timoti ɗan’uwanmu, Zuwa ga ikkilisiyar Allah da take a Korint, tare da dukan tsarkaka a ko’ina a Akayya.
- 2 Korintiyawa 1:2kusan 60 M.
Alheri da salama daga Allah Ubanmu da kuma Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
- 2 Korintiyawa 1:3kusan 60 M.
Yabo ya tabbata ga Allah, da Uban Ubangijinmu Yesu Kiristi, Uba mai tausayi, da kuma Allah na dukan ta’aziyya,
- 2 Korintiyawa 1:4kusan 60 M.
wanda yakan yi mana ta’aziyya a cikin dukan wahalolinmu, domin mu kuma mu iya ta’azantar da waɗanda suke cikin kowace irin wahala, da ta’aziyyar da mu kanmu muka samu daga Allah.
- 2 Korintiyawa 1:5kusan 60 M.
Gama kamar yadda wahalar Kiristi ta cika har tana zuba a cikin rayuwarmu, haka nan kuma ta wurin Kiristi ta’aziyyarmu ta cika har tana zuba.