- English
- King James KJV
- Complete Jewish CJB
- World English WEBM
- Berean Standard BSB
- American Standard ASV
- Geneva GNV
- Young's Literal YLT
- Douay-Rheims DRC
- International
- Shqip ALB
- العربية SVD
- বাংলা BN-IRV
- မြန်မာ Judson
- 简体文 CUV-S
- 繁體中文 CUV-T
- Čeština BKR
- Nederlands STVE
- Français LSG
- Deutsch SCH
- Ελληνικά Vamvas
- ગુજરાતી GU-IRV
- Hausa HCB
- עברית Hebrew
- हिन्दी HCV
- Magyar KAROLI
- Bahasa Indonesia INDO-TB
- Italiano Diodati
- 日本語 Kougo
- 한국어 Korean
- മലയാളം MAL
- मराठी MRCV
- Norsk DNB
- فارسی OPV
- Polski BG
- Português Almeida
- Română Cornilescu
- Русский Synodal
- Español RVG
- Kiswahili Neno
- Svenska SV1917
- Tagalog TAG-ADB
- தமிழ் TCV
- తెలుగు TSA
- ภาษาไทย THAI-KJV
- Українська Ohienko
- Tiếng Việt CADMAN
- Yorùbá YCB
circa AD 48–96
Letters to the Churches
Paul and other apostles write to strengthen, correct, and encourage the scattered churches across the Roman world.
Ayoyi daga wannan lokacin
- 1 Korintiyawa 14:28kusan 59 M.
In babu mai fassara, sai mai magana yă yi shiru a cikin ikkilisiya, yă yi wa kansa magana da kuma Allah.
- 1 Korintiyawa 14:29kusan 59 M.
Annabawa biyu ko uku za su iya yin magana, sauran kuma sai su auna a hankali abin da aka faɗa.
- 1 Korintiyawa 14:30kusan 59 M.
In kuma wahayi ya zo wa wani da yake zaune, sai mai magana na farko yă yi shiru.
- 1 Korintiyawa 14:31kusan 59 M.
Dukanku kuna iya yin annabci bi da bi, domin kowa yă sami koyarwa da ƙarfafawa.
- 1 Korintiyawa 14:32kusan 59 M.
Ruhohin annabawa kuwa suna ƙarƙashin sarrafawar annabawa.
- 1 Korintiyawa 14:33kusan 59 M.
Gama Allah, ba Allah mai sa rikicewa ba ne, sai dai mai salama. Kamar yadda yake a dukan ikkilisiyoyi na tsarkaka.
- 1 Korintiyawa 14:34kusan 59 M.
Ya kamata mata su zauna shiru a cikin ikkilisiyoyi. Ba su da izinin yin magana, sai dai su yi biyayya yadda Doka ta faɗi.
- 1 Korintiyawa 14:35kusan 59 M.
In suna so su yi tambaya game da wani abu, ya kamata su tambayi mazansu a gida, domin abin kunya ne mace tă yi magana a cikin ikkilisiya.
- 1 Korintiyawa 14:36kusan 59 M.
Shin, a kanku ne maganar Allah ta fara? Ko kuma a gare ku ne kaɗai ta iso?
- 1 Korintiyawa 14:37kusan 59 M.
In wani yana tsammani shi annabi ne, ko yana da baiwar ruhaniya, bari yă gane cewa abin da nake rubuta muku umarnin Ubangiji ne.
- 1 Korintiyawa 14:38kusan 59 M.
In ya ƙi kula da wannan, shi ma sai a ƙi kula da shi.
- 1 Korintiyawa 14:39kusan 59 M.
Saboda haka ’yan’uwana, ku yi marmarin yin annabci, kada kuma ku hana magana da harsuna.
- 1 Korintiyawa 14:40kusan 59 M.
Sai dai a yi kome daidai da kuma cikin tsari.
- 1 Korintiyawa 15:1kusan 59 M.
To, ’yan’uwa, ina so in tuna muku da bisharar da na yi muku wa’azinta, wadda kuka karɓa, wadda kuma kuka yanke shawara ku tsaya a kai.
- 1 Korintiyawa 15:2kusan 59 M.
Ta wurin wannan bisharar ce kuka sami ceto, muddin kuna riƙe da wa’azin da na yi muku kam-kam. In ba haka ba, kun gaskata a banza ke nan.
- 1 Korintiyawa 15:3kusan 59 M.
Gama abu farko mafi muhimmancin da na karɓo shi ne na ba ku cewa Kiristi ya mutu domin zunubanmu bisa ga Nassi,
- 1 Korintiyawa 15:4kusan 59 M.
cewa an binne shi an kuma tashe shi a rana ta uku bisa ga Nassi,
- 1 Korintiyawa 15:5kusan 59 M.
cewa ya bayyana ga Bitrus, sa’an nan ga Sha Biyun.
- 1 Korintiyawa 15:6kusan 59 M.
Bayan haka, ya bayyana ga fiye da ɗari biyar daga cikin ’yan’uwa a lokaci guda. Yawancinsu kuwa suna nan da rai, ko da yake waɗansu sun riga sun yi barci.
- 1 Korintiyawa 15:7kusan 59 M.
Sa’an nan ya bayyana ga Yaƙub, sa’an nan ga dukan manzannin,
- 1 Korintiyawa 15:8kusan 59 M.
a ƙarshe duka, ya bayyana a gare ni, kamar wanda an haifa a lokacin da bai kamata ba.
- 1 Korintiyawa 15:9kusan 59 M.
Gama ni ne mafi ƙanƙanta a cikin manzanni, ban kuma isa a kira ni manzo ba, domin na tsananta wa ikkilisiyar Allah.
- 1 Korintiyawa 15:10kusan 59 M.
Amma bisa ga alherin Allah, na zama abin da nake, alherinsa zuwa gare ni kuwa bai zama a banza ba. A’a, na yi aiki fiye da dukansu, duk da haka, ba ni ba ne, sai dai alherin Allah da yake tare da ni ne.
- 1 Korintiyawa 15:11kusan 59 M.
To, ko ni ne, ko su ne, wannan shi ne abin da muke wa’azi, shi ne kuma abin da kuka gaskata.
- 1 Korintiyawa 15:12kusan 59 M.
Amma in ana wa’azi cewa Kiristi ya tashi daga matattu, yaya waɗansu a cikinku suke cewa babu tashin matattu?