- English
- King James KJV
- Complete Jewish CJB
- World English WEBM
- Berean Standard BSB
- American Standard ASV
- Geneva GNV
- Young's Literal YLT
- Douay-Rheims DRC
- International
- Shqip ALB
- العربية SVD
- বাংলা BN-IRV
- မြန်မာ Judson
- 简体文 CUV-S
- 繁體中文 CUV-T
- Čeština BKR
- Nederlands STVE
- Français LSG
- Deutsch SCH
- Ελληνικά Vamvas
- ગુજરાતી GU-IRV
- Hausa HCB
- עברית Hebrew
- हिन्दी HCV
- Magyar KAROLI
- Bahasa Indonesia INDO-TB
- Italiano Diodati
- 日本語 Kougo
- 한국어 Korean
- മലയാളം MAL
- मराठी MRCV
- Norsk DNB
- فارسی OPV
- Polski BG
- Português Almeida
- Română Cornilescu
- Русский Synodal
- Español RVG
- Kiswahili Neno
- Svenska SV1917
- Tagalog TAG-ADB
- தமிழ் TCV
- తెలుగు TSA
- ภาษาไทย THAI-KJV
- Українська Ohienko
- Tiếng Việt CADMAN
- Yorùbá YCB
circa 6 BC – AD 30
The Life of Jesus
The eternal Son of God enters history: born in Bethlehem, baptized in the Jordan, crucified at Golgotha, raised on the third day.
Ayoyi daga wannan lokacin
- Yohanna 15:21kusan 33 M.
Za su yi muku haka saboda sunana, gama ba su san Wannan da ya aiko ni ba.
- Yohanna 15:22kusan 33 M.
Da a ce ban zo na yi musu magana ba, da ba su da zunubi. Yanzu kam, ba su da wata hujja a kan zunubinsu.
- Yohanna 15:23kusan 33 M.
Wanda ya ƙi ni ya ƙi ya ƙi Ubana ma.
- Yohanna 15:24kusan 33 M.
Da a ce ban yi ayyuka a cikinsu waɗanda babu wani da ya taɓa yi ba, da ba su da zunubi. Amma yanzu sun ga waɗannan ayyukan banmamaki, duk da haka sun ƙi ni sun kuma ƙi Ubana.
- Yohanna 15:25kusan 33 M.
Amma wannan ya faru ne domin a cika abin da yake a rubuce cikin Dokarsu cewa, ‘Sun ƙi ni ba dalili.’
- Yohanna 15:26kusan 33 M.
“Sa’ad da Mai Taimako ya zo, wanda zan aiko muku daga wurin Uba, Ruhun gaskiya wanda yake fitowa daga wurin Uba, zai ba da shaida game da ni.
- Yohanna 15:27kusan 33 M.
Ku ma dole ku ba da shaida, domin kun kasance tare da ni tun daga farko.
- Yohanna 16:1kusan 33 M.
“Na faɗa muku wannan duka, domin kada ku bauɗe.
- Yohanna 16:2kusan 33 M.
Za su kore ku daga majami’a; lalle, lokaci yana zuwa da duk wanda ya kashe ku, zai ɗauka yana yin wa Allah hidima ne.
- Yohanna 16:3kusan 33 M.
Za su yi waɗannan abubuwa ne domin ba su san Uba ko ni ba.
- Yohanna 16:4kusan 33 M.
Na faɗa muku wannan, domin in lokacin ya yi, ku tuna na gargaɗe ku. Ban faɗa muku wannan tun da fari ba domin ina tare da ku.
- Yohanna 16:5kusan 33 M.
“Yanzu zan tafi wurin wanda ya aiko ni, duk da haka ba waninku da ya tambaye ni, ‘Ina za ka?’
- Yohanna 16:6kusan 33 M.
Saboda na faɗa waɗannan abubuwa ga shi kun cika da baƙin ciki.
- Yohanna 16:7kusan 33 M.
Amma gaskiya nake gaya muku. Don amfaninku ne zan tafi. Sai ko na tafi, in ba haka ba Mai Taimakon nan ba zai zo muku ba. Amma in na tafi, zan aiko shi gare ku.
- Yohanna 16:8kusan 33 M.
Sa’ad da ya zo kuwa, zai kā da duniya a kan zunubi da adalci da kuma hukunci,
- Yohanna 16:9kusan 33 M.
a kan zunubi, domin mutane ba su gaskata da ni ba;
- Yohanna 16:10kusan 33 M.
a kan adalci, domin zan tafi wurin Uba, inda ba za ku ƙara ganina ba;
- Yohanna 16:11kusan 33 M.
a kan hukunci kuma, domin an yanke hukunci a kan mai mulkin duniyan nan.
- Yohanna 16:12kusan 33 M.
“Ina da sauran abubuwa da yawa da zan faɗa muku, amma ba za ku iya ɗauka a yanzu ba.
- Yohanna 16:13kusan 33 M.
Amma sa’ad da shi, Ruhun gaskiya ya zo, zai bi da ku zuwa ga dukan gaskiya. Ba zai yi magana don kansa ba; zai faɗi abin da ya ji ne kaɗai, zai kuma faɗa muku abin da bai faru ba tukuna.
- Yohanna 16:14kusan 33 M.
Zai kawo ɗaukaka gare ni ta wurin ɗaukan abin da yake nawa, ya bayyana muku.
- Yohanna 16:15kusan 33 M.
Duk abin da yake na Uba nawa ne. Shi ya sa na ce, ‘Ruhun zai ɗauko daga abin da yake nawa, yă bayyana muku.’ ”
- Yohanna 16:16kusan 33 M.
Yesu ya ci gaba da cewa, “Jim kaɗan, ba za ku ƙara ganina ba, sa’an nan bayan an jima kaɗan kuma, za ku gan ni.”
- Yohanna 16:17kusan 33 M.
A nan fa sai waɗansu almajiransa suka ce wa juna, “Me yake nufi da cewa, ‘Jim kaɗan ba za ku ƙara ganina ba, kuma bayan an jima kaɗan, za ku gan ni,’ da kuma, ‘Domin zan tafi wurin Uba’?”
- Yohanna 16:18kusan 33 M.
Suka yi ta tambaya, “Me yake nufi da ‘jim kaɗan’? Ba mu fahimci abin da yake faɗi ba.”