Skip to content

Bethany

11 verses

31.7700, 35.2600 Duba a Google Maps

Ayoyin da suka ambaci Bethany

  1. Sai ya bar su, ya fita daga birnin ya tafi Betani, inda ya kwana.

  2. Yayinda Yesu yake a Betani, a gidan wani mutumin da ake kira Siman Kuturu,

  3. Sa’ad da suka yi kusa da Urushalima, suka zo Betfaji da Betani wajen Dutsen Zaitun, sai Yesu ya aiki biyu daga cikin almajiransa,

  4. Yesu ya shiga Urushalima ya kuma tafi filin haikali. Ya dudduba kome duka, amma da yake yamma ta yi, sai ya tafi Betani tare da Sha Biyun.

  5. Kashegari, da suke barin Betani, Yesu kuwa ya ji yunwa.

  6. Yayinda yake a Betani, a gidan wani mutumin da ake kira Siman Kuturu, yana cin abinci, sai wata mace ta zo da wani ɗan tulu na turaren alabasta da aka yi da nardi zalla, mai tsadan gaske. Ta fasa tulun, ta kuma zuba turaren a kansa.

  7. Da ya kai kusa da Betfaji da Betani, a tudun da ake kira Dutsen Zaitun, sai ya aiki almajiransa guda biyu, ya ce musu,

  8. Bayan ya kai su waje kusa da Betani, sai ya ɗaga hannuwansa ya sa musu albarka.

  9. To, an yi wani mutum mai suna Lazarus wanda ya yi rashin lafiya. Shi daga Betani ne, ƙauyen su Maryamu da ’yar’uwarta Marta.

  10. Betani bai kai mil biyu ba daga Urushalima,

  11. Kwana shida kafin Bikin Ƙetarewa, sai Yesu ya iso Betani, inda Lazarus yake, wanda Yesu ya tā da daga matattu.