Tsallake zuwa abun ciki

circa AD 48–96

Letters to the Churches

Paul and other apostles write to strengthen, correct, and encourage the scattered churches across the Roman world.

2,767 ayoyi · 21 littattafai da aka rufe

Ayoyi daga wannan lokacin

Tace bisa littafi
  1. Romawa 3:15kusan 60 M.

    “Ƙafafunsu suna saurin kai su zuwa ga zub da jini;

  2. Romawa 3:16kusan 60 M.

    hallaka da baƙin ciki suna ko’ina a hanyoyinsu,

  3. Romawa 3:17kusan 60 M.

    ba su kuma san hanyar salama ba.”

  4. Romawa 3:18kusan 60 M.

    “Babu tsoron Allah a idanunsu.”

  5. Romawa 3:19kusan 60 M.

    Yanzu mun san cewa dukan abin da doka ta ce, tana magana ne ga waɗanda suke ƙarƙarshin doka, saboda a rufe kowane baki; dukan duniya kuma ta ba da lissafin kanta a gaban Allah.

  6. Romawa 3:20kusan 60 M.

    Saboda haka babu wanda Allah zai ce da shi mai adalci ta wurin kiyaye doka kawai; a maimako, ta wurin doka ne muke sane da zunubi.

  7. Romawa 3:21kusan 60 M.

    Amma yanzu an bayyana wani adalci daga Allah, wannan adalcin bai danganta ga doka ba, Doka da Annabawa suna ba da shaida game da wannan adalci.

  8. Romawa 3:22kusan 60 M.

    Wannan adalcin Allah yana zuwa ta wurin bangaskiya a cikin Yesu Kiristi ga dukan waɗanda suka ba da gaskiya ne. Ba bambanci,

  9. Romawa 3:23kusan 60 M.

    gama duka sun yi zunubi suka kuma kāsa ga ɗaukakar Allah,

  10. Romawa 3:24kusan 60 M.

    an kuma kuɓutar da su kyauta ta wurin alherinsa bisa ga aikin fansar da ya zo ta wurin Yesu Kiristi.

  11. Romawa 3:25kusan 60 M.

    Allah ya miƙa Yesu Kiristi a matsayin hadayar kafara, ta wurin bangaskiya cikin jininsa. Ya yi haka domin yă nuna adalcinsa, domin a cikin haƙurinsa bai hukunta zunuban da aka aikata a dā ba

  12. Romawa 3:26kusan 60 M.

    ya yi haka domin yă nuna adalcinsa a wannan lokaci, saboda yă zama mai adalci da mai kuɓutar da waɗanda suke ba da gaskiya a cikin Yesu.

  13. Romawa 3:27kusan 60 M.

    To, me za mu yi taƙama a kai? Babu wani abin da zamu yi taƙama a kai. A kan wace ƙa’ida ce za mu yi taƙama? Ta hanyar bin doka ne? A’a, sai dai ta wurin bangaskiya.

  14. Romawa 3:28kusan 60 M.

    Gama mun tsaya a kan cewa ta wurin bangaskiya ne ake kuɓutar da mutum, ba ta wurin kiyaye doka ba.

  15. Romawa 3:29kusan 60 M.

    Allah ɗin, Allahn Yahudawa ne kaɗai? Shi ba Allahn Al’ummai ba ne? I, shi Allahn Al’ummai ne ma,

  16. Romawa 3:30kusan 60 M.

    da yake Allah ɗaya ne kaɗai, shi kuma zai kuɓutar da masu kaciya bisa ga bangaskiya da kuma marasa kaciya ta wurin wannan bangaskiya ɗin.

  17. Romawa 3:31kusan 60 M.

    To, za mu soke dokar saboda wannan bangaskiyar ne? Ko kaɗan! A maimako, sai ma tabbatar da ita muke yi.

  18. Romawa 4:1kusan 60 M.

    To, me za mu ce Ibrahim kakan kakanninmu ya gani game da wannan batu?

  19. Romawa 4:2kusan 60 M.

    In fa da gaske ne Ibrahim ya sami kuɓuta ta wurin ayyuka, yana da abin da zai yin taƙama da shi ke nan, amma ba a gaban Allah ba.

  20. Romawa 4:3kusan 60 M.

    Me Nassin ya ce? “Ibrahim ya gaskata Allah, aka kuma lissafta wannan adalci ne a gare shi.”

  21. Romawa 4:4kusan 60 M.

    To, sa’ad da mutum ya yi aiki, ba a lissafta ladan aikinsa a matsayin kyauta, sai dai a matsayin hakkinsa.

  22. Romawa 4:5kusan 60 M.

    Amma fa, game da mutumin da ba ya aiki sai dai dogara ga Allah wanda yake kuɓutar da masu mugunta, akan lissafta bangaskiyarsa a matsayin adalci ne.

  23. Romawa 4:6kusan 60 M.

    Dawuda ya faɗi haka sa’ad da ya yi magana game da albarkar da aka yi wa mutumin da Allah ya lissafta adalci a gare shi, ba don yă yi ayyuka ba.

  24. Romawa 4:7kusan 60 M.

    “Masu albarka ne waɗanda aka gafarta laifofinsu, waɗanda aka kuma rufe zunubansu.

  25. Romawa 4:8kusan 60 M.

    Mai albarka ne mutumin da Ubangiji ba zai taɓa lissafta zunubansa ba.”