Tsallake zuwa abun ciki

circa 2100–1900 BC

Abraham: The Covenant

God calls Abram from Ur, establishes an everlasting covenant, and promises a son through whom all nations will be blessed.

394 ayoyi · 1 littafi da aka rufe

Ayoyi daga wannan lokacin

  1. Farawa 24:58kusan 1857 K.H.

    Saboda haka suka kira Rebeka suka ce mata, “Za ki tafi tare da mutumin nan?” Sai ta ce, “Zan tafi.”

  2. Farawa 24:59kusan 1857 K.H.

    Saboda haka suka sallame Rebeka, ’yar’uwarsu, duk da uwar goyonta da bawan Ibrahim da mutanensa.

  3. Farawa 24:60kusan 1857 K.H.

    Suka kuma albarkaci Rebeka suka ce mata, “’Yar’uwarmu, bari ki zama mahaifiyar dubu dubbai, bari zuriyarki su mallaki ƙofofin abokan gābansu.”

  4. Farawa 24:61kusan 1857 K.H.

    Sa’an nan Rebeka da bayinta mata suka shirya suka hau raƙumansu suka koma tare da mutumin. Da haka bawan ya ɗauki Rebeka ya tafi.

  5. Farawa 24:62kusan 1857 K.H.

    Ishaku kuwa ya zo daga Beyer-Lahai-Royi, gama yana zama a Negeb.

  6. Farawa 24:63kusan 1857 K.H.

    Wata rana da yamma ya fita zuwa fili domin yă yi tunani, sa’ad da ya ɗaga ido, sai ya ga raƙuma suna zuwa.

  7. Farawa 24:64kusan 1857 K.H.

    Rebeka ma ta ɗaga ido sai ta ga Ishaku. Ta sauka daga raƙuminta da sauri,

  8. Farawa 24:65kusan 1857 K.H.

    ta ce wa bawan, “Wane ne mutumin can a fili, da yake zuwa yă tarye mu?” Bawan ya ce, “Maigidana ne.” Saboda haka ta ɗauki mayafinta to rufe kanta.

  9. Farawa 24:66kusan 1857 K.H.

    Sai bawan ya faɗa wa Ishaku duk abin da ya yi.

  10. Farawa 24:67kusan 1857 K.H.

    Ishaku ya kawo ta cikin tentin mahaifiyarsa Saratu, ya kuma auri Rebeka. Ta haka ta zama matarsa, ya kuwa ƙaunace ta; Ishaku kuma ya ta’azantu bayan rasuwar mahaifiyarsa.

  11. Farawa 25:1kusan 1853 K.H.

    Ibrahim ya auro wata mace, mai suna Ketura.

  12. Farawa 25:2kusan 1852 K.H.

    Ta haifa masa Zimran, Yokshan, Medan, Midiyan, Ishbak da Shuwa.

  13. Farawa 25:3kusan 1824 K.H.

    Yokshan shi ne mahaifin Sheba da Dedan. Zuriyar Dedan su ne mutanen Ashur, da mutanen Letush, da kuma mutanen Lewummin.

  14. Farawa 25:4kusan 1804 K.H.

    ’Ya’yan Midiyan maza su ne, Efa, Efer, Hanok, Abida, da kuma Elda’a. Dukan waɗannan zuriyar Ketura ce.

  15. Farawa 25:5kusan 1829 K.H.

    Ibrahim ya bar wa Ishaku kome da ya mallaka.

  16. Farawa 25:6kusan 1829 K.H.

    Amma yayinda Ibrahim yake da rai, ya ba wa ’ya’yan ƙwarƙwaransa maza kyautai, ya kuma sallame su daga ɗansa Ishaku zuwa ƙasashen gabas.

  17. Farawa 25:7kusan 1821 K.H.

    Duka-duka, Ibrahim ya yi shekara ɗari da saba’in da biyar.

  18. Farawa 25:8kusan 1821 K.H.

    Sa’an nan Ibrahim ya ja numfashinsa na ƙarshe, ya kuma mutu da kyakkyawar tsufa, tsoho da kuma shekaru masu yawa; aka kuma tara shi ga mutanensa.

  19. Farawa 25:9kusan 1821 K.H.

    ’Ya’yansa maza kuwa Ishaku da Ishmayel suka binne shi cikin kogon Makfela, kusa da Mamre, a cikin filin Efron ɗan Zohar mutumin Hitti,

  20. Farawa 25:10kusan 1821 K.H.

    filin da Ibrahim ya saya daga Hittiyawa. A nan aka binne Ibrahim tare da matarsa Saratu.

  21. Farawa 25:11kusan 1821 K.H.

    Bayan rasuwar Ibrahim, Allah ya albarkaci ɗansa Ishaku wanda a lokacin yana zama kusa da Beyer-Lahai-Royi.

  22. Farawa 25:12kusan 1821 K.H.

    Waɗannan su ne zuriyar Ishmayel ɗan Ibrahim, wanda Hagar mutuniyar Masar, baranyar Saratu, ta haifa wa Ibrahim.

  23. Farawa 25:13kusan 1821 K.H.

    Ga jerin sunayen ’ya’yan Ishmayel maza bisa ga haihuwarsu, Nebayiwot ɗan farin Ishmayel, Kedar, Adbeyel, Mibsam,

  24. Farawa 25:14kusan 1821 K.H.

    Mishma, Duma, Massa,

  25. Farawa 25:15kusan 1821 K.H.

    Hadad, Tema, Yetur, Nafish da Kedema.