Tsallake zuwa abun ciki

Ayoyin Littafi Mai Tsarki game da Faith

543 ayoyi · 124 fannoni

Mahimman ayoyin Littafi Mai Tsarki

Tace bisa littafi
  1. Ya tsaya cik, amma ban iya sani ko mene ne ba. Wani abu ya tsaya a gabana, na kuma ji murya.

  2. ‘Ko zai yiwu mutum yă fi Allah adalci, ko kuma mutum yă fi wanda ya halicce shi tsarki?

  3. In Allah bai yarda da bayinsa ba, in ya sami mala’ikunsa da laifi,

  4. to, su wane ne mutane masu zama a gidan da aka yi da laka, waɗanda da ƙura aka yi harsashensu, waɗanda za a iya murƙushe su kamar asu!

  5. Tsakanin safe da yamma mai yiwuwa ne ragargaza su; farat ɗaya, su mutu har abada.

  6. Ba a tuge igiyar tentinsu, don su mutu ba tare da hikima ba?’

  7. “Amma da a ce ni ne, da zan roƙi Allah; zan gaya masa damuwata.

  8. Yana yin abubuwan al’ajabi waɗanda ba a ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a ƙirgawa.

  9. Ko da zai kashe ni ne, begena a cikinsa zai kasance; ba shakka zan kāre kaina a gabansa

  10. lalle wannan zai kawo mini kuɓuta gama ba wani marar tsoron Allah da zai iya zuwa wurinsa!

  11. Na san wanda zai fanshe ni yana nan da rai, kuma a ƙarshe zai tsaya a kan duniya.

  12. Kuma bayan an hallaka fatata, duk da haka a cikin jiki zan ga Allah.

  13. Zan gan shi da kaina da idanuna, Ni, ba wani ba ne. Zuciyata ta cika da wannan tunani!

  14. Na kwanta na yi barci; na kuma farka, gama Ubangiji yana kiyaye ni.

  15. Ba zan ji tsoro ko dubu goma suka ja dāgā gāba da ni a kowane gefe ba.

  16. Ku tafi daga gare ni, dukanku masu aikata mugunta, gama Ubangiji ya ji kukata.

  17. Ubangiji ya ji kukata saboda jinƙansa; Ubangiji ya karɓi addu’ata.

  18. Abokan gābana sun ja da baya; suka yi tuntuɓe suka hallaka a gabanka.

  19. Gama ka tabbata da gaskiyata da kuma abin da nake yi; ka zauna a kujerarka, kana yin shari’a da adalci.

  20. Ubangiji shi ne mafakan waɗanda ake danniya, mafaka a lokutan wahala.

  21. Waɗanda suka san sunanka za su dogara da kai, gama kai, Ubangiji, ba ka taɓa yashe waɗanda suke nemanka ba.

  22. Miktam ne na Dawuda. Ka kiyaye ni, ya Allah, gama a cikinka nake samun mafaka.

  23. Na ce wa Ubangiji, “Kai ne shugabana; in ba tare da kai ba, ba ni da wani abu mai kyau.”

  24. Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Ya rera ta ga Ubangiji kalmomin wannan waƙa sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa da kuma daga hannun Shawulu, ya ce, Ina ƙaunarka, ya Ubangiji, ƙarfina.

  25. Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona; Allahna shi ne dutsena, a gare shi nake neman mafaka. Shi ne garkuwata da ƙahon cetona, mafakata.