Tsallake zuwa abun ciki

Ayoyin Littafi Mai Tsarki game da Afflictions and Adversities

526 ayoyi · 5 fannoni

Mahimman ayoyin Littafi Mai Tsarki

Tace bisa littafi
  1. Ubangiji yakan ji masu bukata ba ya kuwa ƙyale kamammun mutanensa.

  2. Ko da yake ka sa na ga wahaloli, masu yawa da kuma masu ɗaci, za ka sāke mayar mini da rai; daga zurfafan duniya za ka sāke tā da ni.

  3. Jikina da zuciyata za su iya raunana, amma Allah ne ƙarfin zuciyata da kuma rabona har abada.

  4. fushin Allah ya ƙuna a kansu; ya karkashe waɗanda suka fi ƙiba a cikinsu, yana yankan matasan Isra’ila.

  5. Duk da haka, suka ci gaba da yin zunubi; duk da abubuwan banmamakinsa, ba su gaskata ba.

  6. Saboda haka ya sa kwanakinsu suka ƙare a banza shekarunsu kuma cikin masifa.

  7. A duk sa’ad da Allah ya kashe su, sai su neme shi; sukan juyo a natse gare shi.

  8. Ka sa ni a ramin da yake can ƙasa cikin zurfafa mafi duhu.

  9. Hasalarka tana da nauyi a kaina; ka turmushe ni da dukan raƙumanka. Sela

  10. Hasalarka ta sha kaina; razanarka ta hallaka ni.

  11. Amma ka ƙi, ka yi ƙyama ka kuma yi fushi sosai da shafaffenka.

  12. Ka soke alkawarin da ka yi da bawanka ka kuma ƙazantar da rawaninsa a ƙura.

  13. Ka rurrushe dukan katangansa ka sa kagaransa suka zama kufai.

  14. Dukan waɗanda suka wuce sun washe shi; ya zama abin dariya wajen maƙwabtansa.

  15. Ka ɗaukaka hannun dama na maƙiyansa; ka sa dukan abokan gābansa suna farin ciki.

  16. Ka juye bakin takobinsa ba ka kuma taimake shi a cikin yaƙi ba.

  17. Ka kawo ƙarshen darajarsa ka kuma jefar da kursiyinsa ƙasa.

  18. Ka rage kwanakin ƙuruciyarsa; ka rufe shi da mayafin kunya. Sela

  19. An cinye mu ta wurin fushinka mun kuma razana ta wurin hasalarka.

  20. Faranta mana zuciya kamar yawan kwanakin da muka sha azaba, kamar yawan shekarun da muka ga wahala.

  21. Mai albarka ne mutumin da ka yi masa horo, ya Ubangiji, mutumin da ka koyar daga dokarka;

  22. kana ba shi sauƙi a lokacin wahala, sai har an haƙa rami wa mugaye.

  23. Da ba don Ubangiji ya yi mini taimako ba, da tuni na zauna shiru a wurin mutuwa.

  24. Sa’ad da na ce, “Ƙafata na santsi,” ƙaunarka, ya Ubangiji, ta riƙe ni.

  25. Sa’ad da alhini ya yi yawa a cikina, ta’aziyyarka ta kawo farin ciki wa raina.