Skip to content

Ayoyin Littafi Mai Tsarki game da Wicked

724 ayoyi · 18 fannoni

Mahimman ayoyin Littafi Mai Tsarki

Tace bisa littafi
  1. Sau nawa suke zama kamar tattaka a iska, ko kuma kamar ƙura da iskar hadari take kwashewa?

  2. An ce ‘Allah yana tara wa ’ya’yan mutum horon da zai ba mutumin.’ Bari yă ba mutumin horo don yă san ya yi haka!

  3. Bari idanunsa su ga yadda zai hallaka; bari yă sha daga fushin Maɗaukaki.

  4. Ko zai damu da iyalin da ya bari a baya sa’ad da kwanakinsa suka ƙare?

  5. “Wani zai iya koya wa Allah ilimi tun da yana shari’anta har da waɗanda suke manya masu iko?

  6. Wani mutum zai mutu cikin jin daɗi da kwanciyar hankali,

  7. jikinsa ɓulɓul, ƙasusuwansa da alamar ƙarfi.

  8. Wani kuma zai mutu cikin ɗacin rai, bai taɓa jin daɗin wani abu mai kyau ba.

  9. Dukansu kuwa za a bizne su a ƙasa, kuma tsutsotsi za su cinye su.

  10. “Na san duk abin da kuke tunani, yadda za ku saɓa mini.

  11. Kuna cewa, ‘Yanzu ina gidan babban mutumin nan, tenti wurin da mugaye suke zama?’

  12. Ba ku taɓa tambayar waɗanda suke tafiya ba? Ba ku kula da labaransu,

  13. cewa an kāre mugu daga ranar bala’i, an kāre shi daga ranar fushi?

  14. Wane ne yake gaya masa abin da ya yi? Wane ne yake rama abin da ya yi?

  15. Za a bizne shi a kabari, a kuma yi tsaron kabarinsa.

  16. Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali; dukan jama’a suna binsa, da yawa kuma suna gabansa.

  17. Ba muguntarka ce ta yi yawa ba? Ba zunubanka ne ba iyaka ba?

  18. “Ka miƙa kanka ga Allah ka samu salamarsa; ta haka ne arziki zai zo maka.

  19. Ka bi umarnin da zai fito daga bakinsa kuma ka riƙe maganarsa a cikin zuciyarka.

  20. In ka komo ga Maɗaukaki, za ka warke. In ka kawar da mugunta daga cikin gidanka.

  21. Ka jefar da zinariyarka a ƙasa, ka jefar da zinariyar Ofir da ka fi so a cikin duwatsu,

  22. sa’an nan ne Maɗaukaki zai zama zinariyarka, zai zama azurfa mafi kyau a wurinka.

  23. Ba shakka a lokacin ne za ka sami farin ciki daga wurin Maɗaukaki, ku kuma ɗaga idanunku ga Allah

  24. Za ka yi addu’a zuwa gare shi, zai kuwa ji ka, kuma za ka cika alkawuranka.

  25. Abin da ka zaɓa za ka yi za ka yi nasara a ciki, haske kuma zai haskaka hanyarka.