- English
- King James KJV
- Complete Jewish CJB
- World English WEBM
- Berean Standard BSB
- American Standard ASV
- Geneva GNV
- Young's Literal YLT
- Douay-Rheims DRC
- International
- Shqip ALB
- العربية SVD
- বাংলা BN-IRV
- မြန်မာ Judson
- 简体文 CUV-S
- 繁體中文 CUV-T
- Čeština BKR
- Nederlands STVE
- Français LSG
- Deutsch SCH
- Ελληνικά Vamvas
- ગુજરાતી GU-IRV
- Hausa HCB
- עברית Hebrew
- हिन्दी HCV
- Magyar KAROLI
- Bahasa Indonesia INDO-TB
- Italiano Diodati
- 日本語 Kougo
- 한국어 Korean
- മലയാളം MAL
- मराठी MRCV
- Norsk DNB
- فارسی OPV
- Polski BG
- Português Almeida
- Română Cornilescu
- Русский Synodal
- Español RVG
- Kiswahili Neno
- Svenska SV1917
- Tagalog TAG-ADB
- தமிழ் TCV
- తెలుగు TSA
- ภาษาไทย THAI-KJV
- Українська Ohienko
- Tiếng Việt CADMAN
- Yorùbá YCB
Ayoyin Littafi Mai Tsarki game da Idolatry
Mahimman ayoyin Littafi Mai Tsarki
Ko ma yayinda suke a masarautarsu, suna jin daɗin girmar kyautatawarka gare su, cikin ƙasar mai girma, da kuma mai fāɗin da ka ba su, ba su bauta maka ko su juye daga mugayen hanyoyinsu ba.
“Amma duba, mu bayi ne a yau, bayi a ƙasar da ka ba kakanninmu don su ci amfaninta da kuma waɗansu abubuwa masu kyau da take bayarwa.
Saboda zunubanmu, yalwar girbin da muke samu yana tafiya wurin sarakunan da ka sa a kanmu. Suna mulki bisa jikunanmu, da bisa garkenmu yadda suka ga dama. Muna cikin baƙin ciki.
Suka ba shi haushi da masujadansu na kan tudu; suka tayar da kishinsa da gumakansu.
Sa’ad da Allah ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; ya ƙi Isra’ila gaba ɗaya.
Ya yashe tabanakul na Shilo, tentin da ya kafa a cikin mutane.
Ya aika da akwatin alkawarin ƙarfinsa zuwa bauta, darajarsa zuwa cikin hannuwan abokin gāba.
Ya ba da mutanensa ga takobi; ya yi fushi ƙwarai da gādonsa.
Wuta ta cinye matasansu maza, ’yan matansu kuma ba su da waƙoƙin aure;
aka karkashe firistocinsu, gwaurayensu kuwa ba su iya makoki ba.
Ba su hallakar da mutanen yadda Ubangiji ya umarce su ba,
amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
Suka miƙa ’ya’yansu maza hadaya ’yan matansu kuma ga aljanu.
Suka zub da jini marar laifi, jinin ’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
Amma gumakansu azurfa da zinariya ne, da hannuwan mutane suka yi.
Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
suna da kunnuwa, amma ba sa ji, hanci, amma ba sa jin ƙanshi
suna da hannuwa, amma ba sa iya taɓa kome, ƙafafu, amma ba sa iya tafiya; ba sa iya ce wani abu da maƙogwaronsu.
Masu yinsu za su zama kamar su, haka kuma zai kasance da duk wanda ya dogara da su.
Gumakan al’ummai azurfa ne da zinariya, da hannuwan mutane suka yi.