Tsallake zuwa abun ciki

circa 1010–970 BC

The Reign of David

David unites the tribes, conquers Jerusalem, and establishes Israel's golden age—even through deep personal failure.

1,230 ayoyi · 2 littattafai da aka rufe

Ayoyi daga wannan lokacin

Tace bisa littafi
  1. 2 Sama’ila 5:16kusan 1048 K.H.

    Elishama, Eliyada da Elifelet.

  2. 2 Sama’ila 5:17kusan 1048 K.H.

    Da Filistiyawa suka ji labari an shafe Dawuda sarki a bisa Isra’ila, sai suka haura da ƙarfi sosai don su nema shi, amma Dawuda ya ji labarin sai ya gangara zuwa mafaka.

  3. 2 Sama’ila 5:18kusan 1048 K.H.

    To, fa, Filistiyawa suka zo suka baje ko’ina a cikin Kwarin Refayim;

  4. 2 Sama’ila 5:19kusan 1048 K.H.

    saboda haka Dawuda ya nemi nufin Ubangiji ya ce, “In tafi in kai wa Filistiya hari? Za ka bashe su a hannuna?” Ubangiji ya amsa masa ya ce, “Je ka, gama tabbatacce zan bashe Filistiyawa a hannunka.”

  5. 2 Sama’ila 5:20kusan 1048 K.H.

    Saboda haka Dawuda ya tafi Ba’al-Ferazim, a can ya ci su da yaƙi. Sai ya ce, “Kamar yadda ruwa yakan fasu, haka Ubangiji ya kakkarya abokan gābana a gabana.” Saboda haka aka kira wurin Ba’al-Ferazim.

  6. 2 Sama’ila 5:21kusan 1048 K.H.

    Filistiyawa suka bar gumakansu a can, Dawuda da mutanensa kuwa suka kwashe su.

  7. 2 Sama’ila 5:22kusan 1048 K.H.

    Har yanzu Filistiyawa suka sāke haurawa suka bazu a Kwarin Refayim;

  8. 2 Sama’ila 5:23kusan 1048 K.H.

    saboda haka Dawuda ya nemi nufin Ubangiji, ya kuwa ce, “Kada ka haura kai tsaye, amma ka kewaya ta bayansu ka fāɗa musu a gaban itatuwan balsam.

  9. 2 Sama’ila 5:24kusan 1048 K.H.

    Da zarar ka ji tafiya kamar na takawar sojoji tana a bisan itatuwan balsam, sai ka yi maza, gama wannan alama ce cewa Ubangiji ya sha gabanka don yă karkashe sojojin Filistiyawa.”

  10. 2 Sama’ila 5:25kusan 1048 K.H.

    Saboda haka Dawuda ya aikata yadda Ubangiji ya umarce shi, ya kuma karkashe Filistiyawa tun daga Geba har zuwa Gezer.

  11. 2 Sama’ila 6:1kusan 1042 K.H.

    Dawuda ya sāke tattara zaɓaɓɓun mutanen Isra’ila, dubu talatin.

  12. 2 Sama’ila 6:2kusan 1042 K.H.

    Shi, da dukan mutanensa suka tashi daga Ba’ala-Yahuda don su hauro da akwatin alkawarin Allah, wanda ake kira da SunanUbangiji Maɗaukaki, wanda yake zama a tsakanin kerubobin da suke a kan akwatin alkawarin.

  13. 2 Sama’ila 6:3kusan 1042 K.H.

    Suka ɗauko akwatin alkawarin Allah a sabuwar keken yaƙi, suka kawo shi daga gidan Abinadab, wanda yake bisa tudu. Uzza da Ahiyo, ’ya’yan Abinadab maza, suka bi da keken yaƙin da akwatin alkawarin Allah yake ciki suka bi da keken yaƙin

  14. 2 Sama’ila 6:4kusan 1042 K.H.

    da akwatin alkawarin Allah yake ciki. Ahiyo kuwa yana tafiya a gaban Abinadab.

  15. 2 Sama’ila 6:5kusan 1042 K.H.

    Dawuda da dukan gidan Isra’ila suka yi biki sosai da dukan ƙarfinsu a gaban Ubangiji, da waƙoƙi, da molaye, da garayu, da ganguna, da kacau-kacau da kuma kuge.

  16. 2 Sama’ila 6:6kusan 1042 K.H.

    Da suka kai masussukar Nakon, sai Uzza ya miƙa hannu don yă riƙe akwatin alkawarin Allah, gama shanun sun yi tuntuɓe.

  17. 2 Sama’ila 6:7kusan 1042 K.H.

    Fushin Ubangiji kuwa ya ƙuna a kan Uzza domin aikin rashin bangirma, saboda haka Allah ya buge shi ya kuma mutu a can kusa da akwatin alkawarin Allah.

  18. 2 Sama’ila 6:8kusan 1042 K.H.

    Ran Dawuda ya ɓace gama fushin Ubangiji ya ɓarke a kan Uzza. Shi ya sa har wa yau ana kira wurin Ferez Uzza.

  19. 2 Sama’ila 6:9kusan 1042 K.H.

    Dawuda ya ji tsoron Ubangiji a ranar, sai ya ce, “Yaya akwatin alkawarin Ubangiji zai iya zuwa wurina?”

  20. 2 Sama’ila 6:10kusan 1042 K.H.

    Bai so yă ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji yă kasance tare da shi a Birnin Dawuda ba. A maimakon haka sai ya kai shi gidan Obed-Edom mutumin Gat.

  21. 2 Sama’ila 6:11kusan 1042 K.H.

    Akwatin Alkawarin Ubangiji ya kasance a gidan Obed-Edom mutumin Gat har tsawon wata uku, Ubangiji kuwa ya albarkace shi da dukan iyalinsa.

  22. 2 Sama’ila 6:12kusan 1042 K.H.

    To, sai aka faɗa wa Sarki Dawuda cewa, “Ubangiji ya sa wa gidan Obed-Edom albarka da dukan abin da yake da shi, saboda akwatin alkawarin Allah.” Saboda haka sai Dawuda ya gangara ya hauro da akwatin alkawarin Allah daga gidan Obed-Edom zuwa Birnin Dawuda da farin ciki.

  23. 2 Sama’ila 6:13kusan 1042 K.H.

    Sa’ad da waɗanda suke ɗaukan akwatin alkawarin Ubangiji suka yi tafiya taki shida, sai yă yi hadayar bijimi da saniya mai ƙiba.

  24. 2 Sama’ila 6:14kusan 1042 K.H.

    Dawuda, sanye da efod lilin, ya yi ta rawa a gaban Ubangiji da dukan ƙarfinsa,

  25. 2 Sama’ila 6:15kusan 1042 K.H.

    yayinda shi da dukan gidan Isra’ila suka hauro da akwatin alkawarin Ubangiji da sowa da kuma busar ƙahoni.