Tsallake zuwa abun ciki

Ayoyin Littafi Mai Tsarki game da Psalms

896 ayoyi · 16 fannoni

Mahimman ayoyin Littafi Mai Tsarki

Tace bisa littafi
  1. Zabura ta Dawuda. Sa’ad da yake a hamadar Yahuda. Ya Allah, kai ne Allahna, da nacewa na neme ka; raina yana ƙishinka, jikina yana marmarinka, cikin busasshiyar ƙasar da ta zozaye inda babu ruwa.

  2. Na gan ka a wuri mai tsarki na kuma dubi ikonka da ɗaukakarka.

  3. Domin ƙaunarka ta fi rai kyau, leɓunana za su ɗaukaka ka.

  4. Zan yabe ka muddin raina, kuma a cikin sunanka zai ɗaga hannuwana.

  5. Raina zai ƙoshi kamar da abinci mafi kyau; da leɓunan rerawa bakina zai yabe ka.

  6. A gadona na tuna da kai; ina tunaninka dukan dare.

  7. Domin kai ne mai taimakona, ina rera a cikin inuwar fikafikanka.

  8. Raina ya manne maka; hannunka na dama yana riƙe da ni.

  9. Su da suke neman raina za su hallaka; za su gangara zuwa zurfafan duniya.

  10. Za a bayar da su ga takobi su kuma zama abincin karnukan jeji.

  11. Amma sarki zai yi farin ciki ga Allah; dukan waɗanda suke rantse da sunan Allah za su yabe shi, amma za a rufe bakunan maƙaryata.

  12. Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ka ji ni, ya Allah, yayinda nake faɗin abin da yake damuna; ka tsare raina daga barazanan abokin gāba.

  13. Ka ɓoye ni daga ƙulle-ƙullen mugaye, daga daure dauren wannan taro masu aikata mugunta.

  14. Sukan wāsa harsunansu kamar takuba su harba kalmominsu kamar kibiyoyi masu kisa.

  15. Sukan yin kwanto su harbi marar laifi; sukan yi harbi nan da nan, ba tsoro.

  16. Sukan ƙarfafa juna a mugayen ƙulle-ƙullensu, sukan yi magana yadda za su ɓoye tarkunansu; su ce, “Wa zai gan su?”

  17. Sukan yi ƙulle-ƙullen rashin adalci su ce, “Mun gama ƙulla cikakkiyar maƙarƙashiya tsab!” Zuciyar mutum da tunaninsa, suna da wuyar ganewa.

  18. Amma Allah zai harbe su da kibiyoyi; nan da nan za a buge su su fāɗi.

  19. Zai juya harshensu a kansu yă kuma kawo su ga hallaka; duk waɗanda suka gan su za su kaɗa kai, suna musu ba’a.

  20. Dukan mutane za su ji tsoro; za su yi shelar ayyukan Allah su kuma yi tunanin abin da ya aikata.

  21. Bari masu adalci su yi farin ciki a cikin Ubangiji su kuma nemi mafaka a gare shi; bari dukan masu gaskiya a zuciya su yabe shi!

  22. Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Wata waƙa. Yabo ya dace da kai, ya Allah, a Sihiyona; a gare ka za mu cika alkawuranmu

  23. Ya kai wanda yake jin addu’a a gare ka dukan mutane za su zo.

  24. Sa’ad da zunubai suka sha ƙarfinmu, ka gafarta laifofinmu.

  25. Masu albarka ne waɗanda ka zaɓa ka kawo kusa don su zauna a filayenka! Mun cika da abubuwa masu kyau na gidanka, na haikalinka mai tsarki.