Tsallake zuwa abun ciki

Ayoyin Littafi Mai Tsarki game da Psalms

896 ayoyi · 16 fannoni

Mahimman ayoyin Littafi Mai Tsarki

Tace bisa littafi
  1. gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,

  2. gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.

  3. Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.

  4. Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.

  5. Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.

  6. Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.

  7. Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai

  8. ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.”

  9. “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.

  10. Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda

  11. (yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki),

  12. cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu

  13. don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,

  14. rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,

  15. don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,

  16. cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.

  17. “Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,

  18. don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,

  19. saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,

  20. don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”

  21. Ko da yake kun riga kun san duk wannan, ina so in tuna muku cewa Ubangiji ya ceci mutanensa daga Masar, duk da haka daga baya ya hallaka waɗanda ba su ba da gaskiya ba.