Tsallake zuwa abun ciki

Ayoyin Littafi Mai Tsarki game da Psalms: Intercessional Psalms

40 ayoyi · 16 fannoni

Ayoyi game da Intercessional Psalms

  1. Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ubangiji ya amsa maka sa’ad da ka yi kira cikin wahala; bari sunan Allah na Yaƙub yă kiyaye ka.

  2. Bari yă aiko maka da taimako daga wuri mai tsarki yă kuma ba ka gudummawa daga Sihiyona.

  3. Bari yă tuna da dukan sadakokinka yă kuma karɓi hadayunka na ƙonawa. Sela

  4. Bari yă biya maka bukatan ranka yă kuma sa dukan shirye-shiryenka su yi nasara.

  5. Za mu yi sowa ta farin ciki sa’ad da ka yi nasara mu kuma ɗaga tutotinmu a cikin sunan Allahnmu. Bari Ubangiji yă biya maka dukan bukatunka.

  6. Yanzu na san cewa, Ubangiji yakan cece shafaffensa. Yakan amsa masa daga samansa mai tsarki da ikon ceto na hannun damansa.

  7. Waɗansu sun dogara a kekunan yaƙi waɗansu kuma a dawakai, amma mu, mun dogara a cikin sunan Ubangiji Allahnmu.

  8. Za a durƙusar da su, su kuma fāɗi, amma mu za mu tashi mu tsaya daram.

  9. Ya Ubangiji, ka ba da nasara ga sarki! Ka amsa mana sa’ad da muka yi kira!

  10. Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Tare da kayan kiɗi masu tsirkiya. Zabura. Waƙa. Bari Allah yă yi mana alheri yă kuma albarkace mu yă kuma sa fuskarsa ta haskaka a kanmu, Sela

  11. don a san hanyoyinka a duniya, cetonka kuma a cikin dukan al’ummai.

  12. Bari mutane su yabe ka, ya Allah; bari dukan mutane su yabe ka.

  13. Bari al’ummai su yi murna su kuma rera don farin ciki, gama kana mulkin mutanenka da adalci kana kuma bi da al’umman duniya. Sela

  14. Bari mutane su yabe ka, ya Allah; bari dukan mutane su yabe.

  15. Sa’an nan ƙasa za tă ba da girbinta Allah kuma, Allahnmu, zai albarkace mu.

  16. Allah yă sa mana albarka, dukan iyakar duniya kuma su ji tsoronsa.

  17. Waƙar haurawa. Ta Dawuda. Na yi farin ciki tare da waɗanda suka ce da ni, “Bari mu tafi gidan Ubangiji.”

  18. Ƙafafunmu suna tsaye a ƙofofinki, ya Urushalima.

  19. An gina Urushalima kamar birnin da aka yi a harhaɗe wuri guda.

  20. A can ne kabilu suke haurawa, kabilan Ubangiji, don su yabi sunan Ubangiji bisa ga farillan da aka ba wa Isra’ila.

  21. A can kursiyoyin shari’a yake tsaye, kursiyoyin gidan Dawuda.

  22. Ku yi addu’a don salamar Urushalima, “Bari waɗanda suke ƙaunarki su zauna lafiya.

  23. Bari salama ta kasance a katangarki zaman lafiya kuma a fadodinki.”

  24. Saboda ’yan’uwana da kuma abokaina, zan ce, “Salama tă kasance tare da ke.”

  25. Saboda gidan Ubangiji Allahnmu, zan nemi wadatarki.