Tsallake zuwa abun ciki

Ayoyin Littafi Mai Tsarki game da Patriotism

63 ayoyi · 1 fanni

Mahimman ayoyin Littafi Mai Tsarki

Tace bisa littafi
  1. Ku yi addu’a don salamar Urushalima, “Bari waɗanda suke ƙaunarki su zauna lafiya.

  2. Bari salama ta kasance a katangarki zaman lafiya kuma a fadodinki.”

  3. Bari Ubangiji ya albarkace ka daga Sihiyona dukan kwanakin ranka; bari ka ga wadatar Urushalima,

  4. bari kuma ka rayu ka ga ’ya’ya ’ya’yanka. Salama tă kasance tare da Isra’ila.

  5. A bakin kogunan Babilon muka zauna muka yi kuka sa’ad da muka tuna da Sihiyona.

  6. A can a kan rassan itatuwa muka rataye garayunmu,

  7. gama a can masu kamunmu suka sa mu yi waƙoƙi, masu ba mu azaba suka nema waƙoƙin farin ciki; suka ce, “Ku rera mana ɗaya daga cikin waƙoƙin Sihiyona!”

  8. Yaya za mu rera waƙoƙin Ubangiji a baƙuwar ƙasa?

  9. In na manta da ke, ya Urushalima, bari hannuna na dama manta da iyawarsa.

  10. Bari harshena yă manne wa rufin bakina in ban tuna da ke ba, in ban so Urushalima farin cikin mafi girma ba.

  11. Saboda Sihiyona ba zan yi shiru ba, saboda Urushalima ba zan huta ba, sai adalcinta ya haskaka kamar hasken safiya, cetonta kuma ya haskaka kamar fitila mai haske.

  12. Sukan ɗaura mikin mutanena sai ka ce mikin ba shi da matsala. Suna cewa, “Lafiya, Lafiya,” alhali kuwa ba lafiya.

  13. Da yake an ragargazar da mutanena, an ragargaza ni ke nan; na yi kuka, tsoro ya kama ni.

  14. Ba magani ne a Gileyad? Ba likita ne a can? To, me ya sa ba warkarwa wa raunin mutanena?

  15. Da ma kaina maɓulɓulan ruwa ne idanuna kuma maɓulɓulan hawaye! Da sai in yi kuka dare da rana saboda mutanena da aka kashe.

  16. Da ma a hamada ina da wurin da matafiye za su sauka, don in bar mutanena in tafi in bar su; gama dukansu mazinata ne, taron mutane marasa aminci.

  17. Ka tuna, ya Ubangiji, abin da ya faru da mu; duba, ka ga kunyar da muka sha.

  18. An ba wa baƙi gādonmu, gidajenmu kuma aka ba bare.

  19. Mun zama marayu marasa ubanni, uwayenmu kamar gwauraye.

  20. Dole mu sayi ruwan da muke sha; sai mun biya mu sami itace.

  21. Masu fafararmu sun kusa kama mu; mun gaji kuma ba dama mu huta.

  22. Mun miƙa kanmu ga Masar da Assuriya don mu sami isashen abinci.

  23. Kakanninmu sun yi zunubi kuma ba sa nan yanzu, mu ne aka bari muna shan hukuncinsu.

  24. Bayi suna mulki a kanmu, kuma ba wanda zai ’yantar da mu daga hannuwansu.

  25. Muna samun burodi a bakin rayukanmu domin takobin da yake a jeji.