circa 6 BC – AD 30
The Life of Jesus
The eternal Son of God enters history: born in Bethlehem, baptized in the Jordan, crucified at Golgotha, raised on the third day.
Ayoyi daga wannan lokacin
- Markus 1:30kusan 27 M.
Surukar Siman tana kwance da zazzaɓi, sai suka gaya wa Yesu game da ita.
- Markus 1:31kusan 27 M.
Sai ya je wajenta, ya kama hannunta, ya ɗaga ta. Zazzaɓin kuwa ya sāke ta, ta kuma yi musu hidima.
- Markus 1:32kusan 27 M.
A wannan yamma, bayan fāɗuwar rana, mutane suka kawo wa Yesu dukan marasa lafiya, da masu aljanu.
- Markus 1:33kusan 27 M.
Duk garin ya taru a ƙofar gidan.
- Markus 1:34kusan 27 M.
Yesu kuwa ya warkar da marasa lafiya da yawa da suke da cututtuka iri-iri. Ya kuma fitar da aljanu da yawa, amma bai yarda aljanun suka yi magana ba, don sun san wane ne shi.
- Markus 1:35kusan 27 M.
Da sassafe, tun da sauran duhu, Yesu ya tashi, ya bar gida, ya tafi wani wurin da ba kowa, a can ya yi addu’a.
- Markus 1:36kusan 27 M.
Siman da abokansa suka fita nemansa.
- Markus 1:37kusan 27 M.
Da suka same shi, sai suka ce, “Kowa yana nemanka!”
- Markus 1:38kusan 27 M.
Yesu ya amsa ya ce, “Mu je wani wuri dabam, zuwa ƙauyukan da suke kusa, don in yi wa’azi a can ma. Wannan shi ne dalilin zuwana.”
- Markus 1:39kusan 27 M.
Sai ya tafi ko’ina a Galili, yana wa’azi a majami’unsu, yana kuma fitar da aljanu.
- Markus 1:40kusan 27 M.
Wani mutum mai kuturta ya zo wurinsa, ya durƙusa ya roƙe shi ya ce, “In kana so, za ka iya tsabtacce ni.”
- Markus 1:41kusan 27 M.
Cike da tausayi, sai Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka tsabtacce!”
- Markus 1:42kusan 27 M.
Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi, ya kuma warke.
- Markus 1:43kusan 27 M.
Yesu ya sallame shi nan take, da gargaɗi mai ƙarfi cewa,
- Markus 1:44kusan 27 M.
“Ka lura kada ka gaya wa kowa wannan. Amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayun da Musa ya umarta saboda tsarkakewarka, don yă zama shaida gare su.”
- Markus 1:45kusan 27 M.
A maimakon haka, sai ya fita, ya fara magana a sake, yana baza labarin. Saboda haka, Yesu bai ƙara iya shiga cikin gari a fili ba, sai dai ya kasance a wuraren da ba kowa. Duk da haka, mutane suka yi ta zuwa wurinsa daga ko’ina.
- Markus 2:1kusan 31 M.
Bayan ’yan kwanaki, da Yesu ya sāke shiga Kafarnahum, sai mutane suka ji labarin zuwansa gida.
- Markus 2:2kusan 31 M.
Mutane suka taru da yawa har ma babu wuri, ko a bakin ƙofa ma, sai ya yi musu wa’azin bishara.
- Markus 2:3kusan 31 M.
Waɗansu mutum huɗu suka zo wajensa ɗauke da wani shanyayye.
- Markus 2:4kusan 31 M.
Da ba su iya kai shi wurin Yesu ba, saboda taron, sai suka buɗe rufin gidan saman, bisa daidai inda Yesu yake. Bayan da suka huda rami, sai suka saukar da shanyayyen, kwance a kan tabarmarsa.
- Markus 2:5kusan 31 M.
Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce wa shanyayyen, “Saurayi, an gafarta zunubanka.”
- Markus 2:6kusan 31 M.
To, waɗansu malaman dokoki da suke zaune a wurin, suka yi tunani a zuciyarsu, suna cewa,
- Markus 2:7kusan 31 M.
“Me ya sa mutumin nan yake magana haka? Yana saɓo! Wane ne zai iya gafarta zunubai, in ba Allah kaɗai ba?”
- Markus 2:8kusan 31 M.
Nan da nan, Yesu ya gane a ruhunsa abin da suke tunani a zuciyarsu, sai ya ce musu, “Me ya sa kuke tunanin waɗannan abubuwa?
- Markus 2:9kusan 31 M.
Wanne ya fi sauƙi, a ce wa shanyayyen, ‘An gafarta zunubanka,’ ko a ce, ‘Tashi, ɗauki tabarmarka ka yi tafiya’?