Tsallake zuwa abun ciki

circa 6 BC – AD 30

The Life of Jesus

The eternal Son of God enters history: born in Bethlehem, baptized in the Jordan, crucified at Golgotha, raised on the third day.

3,779 ayoyi · 4 littattafai da aka rufe

Ayoyi daga wannan lokacin

Tace bisa littafi
  1. Markus 3:7kusan 31 M.

    Yesu da almajiransa suka janye zuwa tafkin, taro mai yawa kuwa daga Galili ya bi shi.

  2. Markus 3:8kusan 31 M.

    Mutane da yawa daga Yahudiya, da Urushalima, da Edom, da kuma yankunan da suke ƙetaren Urdun, da kewayen Taya, da Sidon suka zo wurinsa, don sun ji dukan abubuwan da yake yi.

  3. Markus 3:9kusan 31 M.

    Saboda taron, sai ya ce wa almajiransa su shirya masa ƙaramin jirgin ruwa, don kada mutane su matse shi.

  4. Markus 3:10kusan 31 M.

    Gama ya warkar da mutane da yawa, masu cututtuka suka yi ta ƙoƙarin zuwa gaba, don su taɓa shi.

  5. Markus 3:11kusan 31 M.

    Duk sa’ad da mugayen ruhohi suka gan shi, sai fāɗi a gabansa, su ɗaga murya, su ce, “Kai Ɗan Allah ne.”

  6. Markus 3:12kusan 31 M.

    Amma yakan tsawata musu, kada su shaida ko wane ne shi.

  7. Markus 3:13kusan 31 M.

    Yesu ya hau gefen wani dutse, ya kira waɗanda yake so, suka kuma zo wurinsa.

  8. Markus 3:14kusan 31 M.

    Ya naɗa sha biyu, ya kira su manzanni don su kasance tare da shi, domin kuma yă aike su yin wa’azi,

  9. Markus 3:15kusan 31 M.

    don kuma su sami ikon fitar da aljanu.

  10. Markus 3:16kusan 31 M.

    Ga sha biyun da ya naɗa. Siman (wanda ya ba shi suna Bitrus);

  11. Markus 3:17kusan 31 M.

    Yaƙub ɗan Zebedi da kuma ɗan’uwansa Yohanna (ga waɗannan kuwa ya sa musu suna Buwarnajis, wato, “’ya’yan tsawa”);

  12. Markus 3:18kusan 31 M.

    Andarawus, Filibus, Bartolomeyu, Mattiyu, Toma, Yaƙub ɗan Alfayus, Taddayus, Siman wanda ake kira Zilot,

  13. Markus 3:19kusan 31 M.

    da kuma Yahuda Iskariyot, wanda ya bashe Yesu.

  14. Markus 3:20kusan 31 M.

    Sai Yesu ya shiga wani gida, taro kuma ya sāke haɗuwa, har shi da almajiransa ma ba su sami damar cin abinci ba.

  15. Markus 3:21kusan 31 M.

    Da ’yan’uwansa suka sami wannan labari, sai suka tafi don su dawo da shi, suna cewa, “Ai, ya haukace.”

  16. Markus 3:22kusan 31 M.

    Malaman dokokin da suka zo daga Urushalima suka ce, “Ai, yana da Be’elzebub! Da ikon sarkin aljanu yake fitar da aljanu.”

  17. Markus 3:23kusan 31 M.

    Sai Yesu ya kira su, ya yi musu magana da misalai ya ce, “Yaya Shaiɗan zai fitar da Shaiɗan?

  18. Markus 3:24kusan 31 M.

    In mulki yana gāba da kansa, wannan mulki ba zai tsaya ba.

  19. Markus 3:25kusan 31 M.

    In gida yana gāba da kansa, wannan gida ba zai tsaya ba.

  20. Markus 3:26kusan 31 M.

    In kuwa Shaiɗan yana gāba da kansa, ya kuma rabu biyu, ba zai tsaya ba, ƙarshensa ya zo ke nan.

  21. Markus 3:27kusan 31 M.

    Tabbatacce, ba mai shiga gidan mai ƙarfi yă kwashe dukiyarsa, sai bayan ya daure mai ƙarfin, sa’an nan zai iya yin fashin gidansa.

  22. Markus 3:28kusan 31 M.

    Gaskiya nake gaya muku, za a gafarta duk zunubai da kuma saɓon mutane suka yi.

  23. Markus 3:29kusan 31 M.

    Amma duk wanda ya saɓi Ruhu Mai Tsarki, ba za a taɓa gafara masa ba. Ya aikata madawwamin zunubi ke nan.”

  24. Markus 3:30kusan 31 M.

    Ya faɗi haka domin suna cewa, “Yana da mugun ruhu.”

  25. Markus 3:31kusan 31 M.

    Sai mahaifiyar Yesu tare da ’yan’uwansa suka iso. Suna tsaye a waje, sai suka aiki wani ciki yă kira shi.