Tsallake zuwa abun ciki

circa 6 BC – AD 30

The Life of Jesus

The eternal Son of God enters history: born in Bethlehem, baptized in the Jordan, crucified at Golgotha, raised on the third day.

3,779 ayoyi · 4 littattafai da aka rufe

Ayoyi daga wannan lokacin

Tace bisa littafi
  1. Markus 3:32kusan 31 M.

    Taron yana zaune kewaye da shi, sai suka ce masa, “Mahaifiyarka da ’yan’uwanka suna waje, suna nemanka.”

  2. Markus 3:33kusan 31 M.

    Ya yi tambaya ya ce, “Su wane ne mahaifiyata, da ’yan’uwana?”

  3. Markus 3:34kusan 31 M.

    Sai ya dubi waɗanda suke zaune kewaye da shi ya ce, “Ga mahaifiyata da ’yan’uwana!

  4. Markus 3:35kusan 31 M.

    Duk wanda yake aikata nufin Allah, shi ne ɗan’uwana, da ’yar’uwata, da kuma mahaifiyata.”

  5. Markus 4:1kusan 31 M.

    Har wa yau, Yesu ya fara koyarwa a bakin tafki. Domin taron da yake kewaye da shi mai girma ne sosai, sai ya shiga cikin jirgin ruwa, ya zauna a ciki a tafkin, dukan mutanen kuwa suna a gaɓar ruwan.

  6. Markus 4:2kusan 31 M.

    Ya koya musu abubuwa da yawa da misalai. A koyarwarsa kuwa ya ce,

  7. Markus 4:3kusan 31 M.

    “Ku saurara! Wani manomi ya fita don yă shuka irinsa.

  8. Markus 4:4kusan 31 M.

    Da yana yafa irin, sai waɗansu suka fāɗi a kan hanya, tsuntsaye suka zo suka cinye su.

  9. Markus 4:5kusan 31 M.

    Waɗansu suka fāɗi a wuri mai duwatsu inda babu ƙasa sosai. Nan da nan, suka tsira domin ƙasar ba zurfi.

  10. Markus 4:6kusan 31 M.

    Amma da rana ta taso, sai tsire-tsiren suka ƙone, suka yanƙwane, domin ba su da saiwa.

  11. Markus 4:7kusan 31 M.

    Waɗansu irin suka fāɗi a cikin ƙaya. Da suka yi girma sai ƙaya suka shaƙe su, har ya sa ba su yi ƙwaya ba.

  12. Markus 4:8kusan 31 M.

    Har yanzu, waɗansu irin suka fāɗi a ƙasa mai kyau. Suka tsira, suka yi girma, suka ba da amfani, suka yi riɓi talatin-talatin, waɗansu sittin-sittin, waɗansu kuma ɗari-ɗari.”

  13. Markus 4:9kusan 31 M.

    Sai Yesu ya ce, “Duk mai kunnen ji, yă ji.”

  14. Markus 4:10kusan 31 M.

    Lokacin da yake shi kaɗai, Sha Biyun, da kuma waɗanda suke kewaye da shi, suka tambaye shi game da misalan.

  15. Markus 4:11kusan 31 M.

    Sai ya ce musu, “An ba ku sanin asirin mulkin Allah. Amma ga waɗanda suke waje kuwa, kome sai da misalai.

  16. Markus 4:12kusan 31 M.

    Saboda, “ ‘ko sun dinga duba, ba za su taɓa gane ba, kuma ko su dinga ji, ba za su taɓa fahimta ba, in ba haka ba, mai yiwuwa, su tuba, a gafarta musu!’ ”

  17. Markus 4:13kusan 31 M.

    Sai Yesu ya ce musu, “Ba ku fahimci wannan misali ba? Yaya za ku fahimci wani misali ke nan?

  18. Markus 4:14kusan 31 M.

    Manomi yakan shuka maganar Allah.

  19. Markus 4:15kusan 31 M.

    Waɗansu mutane suna kama da irin da ya fāɗi a kan hanya, inda akan shuka maganar Allah. Da jin maganar, nan da nan sai Shaiɗan yă zo yă ɗauke maganar da aka shuka a zuciyarsu.

  20. Markus 4:16kusan 31 M.

    Waɗansu suna kama da irin da aka shuka a wurare masu duwatsu, sukan ji maganar Allah, sukan kuma karɓe ta nan da nan da farin ciki.

  21. Markus 4:17kusan 31 M.

    Amma da yake ba su da saiwa, ba sa daɗewa. Da wahala ko tsanani ya tashi saboda maganar, nan da nan, sai su ja da baya.

  22. Markus 4:18kusan 31 M.

    Har yanzu, waɗansu kamar irin da aka shuka cikin ƙaya, sukan ji maganar,

  23. Markus 4:19kusan 31 M.

    amma damuwar wannan duniya, da son dukiya, da kuma kwaɗayin waɗansu abubuwa, sukan shiga, su shaƙe maganar, har su mai da ita marar amfani.

  24. Markus 4:20kusan 31 M.

    Waɗansu mutane kuwa suna kama da irin da aka shuka a ƙasa mai kyau, sukan ji maganar Allah, su kuma karɓa, sa’an nan kuma su fid da amfani riɓi talatin-talatin, ko sittin-sittin, ko ɗari-ɗari.”

  25. Markus 4:21kusan 31 M.

    Sai ya ce musu, “Ko kukan kawo fitila ku rufe ta da murfi ko kuma ku sa ta a ƙarƙashin gado ne? Ba kukan sa ta a kan wurin ajiye fitila ba?