Tsallake zuwa abun ciki

circa 800–400 BC

The Hebrew Prophets

God speaks through Isaiah, Jeremiah, and the minor prophets—calling Israel to repentance and foretelling the coming Messiah.

3,706 ayoyi · 14 littattafai da aka rufe

Ayoyi daga wannan lokacin

Tace bisa littafi
  1. Ishaya 2:20kusan 759 K.H.

    A wannan rana mutane za su zubar wa jaba da jamage gumakansu na azurfa da gumakansu na zinariya da suka yi don su bauta musu.

  2. Ishaya 2:21kusan 759 K.H.

    Za su gudu zuwa kogwannin duwatsu da kuma zuwa tsagaggun duwatsu daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa, sa’ad da ya tashi don yă girgiza duniya.

  3. Ishaya 2:22kusan 759 K.H.

    Ku daina dogara ga mutum, wanda numfashi ne kawai yake da shi a hancinsa. Wace daraja gare shi?

  4. Ishaya 3:1kusan 759 K.H.

    Yanzu ka duba fa, Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, yana shirin yă ɗauke kowane tanadi da taimako daga Urushalima da Yahuda dukan tanade-tanaden abinci da kuma dukan tanade-tanaden ruwa,

  5. Ishaya 3:2kusan 759 K.H.

    jarumi, da soja, alƙali da annabi masu duba da dattijo,

  6. Ishaya 3:3kusan 759 K.H.

    shugaban sojojin hamsin da mutum mai makami, mai ba da shawara, gwanin sarrafa abubuwa da mai gwanintan dabo.

  7. Ishaya 3:4kusan 759 K.H.

    “Zan sa ’yan yara su zama shugabanninsu; ’yan yara kurum za su yi mulkinsu.”

  8. Ishaya 3:5kusan 759 K.H.

    Mutane za su zalunci juna mutum da mutum, maƙwabci da maƙwabci. Yara za su rena tsofaffi, ƙasƙantacce zai rena mai daraja.

  9. Ishaya 3:6kusan 759 K.H.

    Mutum zai kama ɗaya daga cikin ’yan’uwansa a gidan mahaifinsa ya ce, “Kana da abin sawa, ka zama shugabanmu; wannan kango kuma yă zama a ƙarƙashinka!”

  10. Ishaya 3:7kusan 759 K.H.

    Amma a ranan nan zai tā da murya ya ce, “Ba ni ba dai. Ba ni da abinci ko abin sawa a gidana; kada ka mai da ni shugaban mutane.”

  11. Ishaya 3:8kusan 759 K.H.

    Urushalima tana tangaɗi, Yahuda yana fāɗuwa; maganganunsu da ayyukansu suna gāba da Ubangiji, suna rena ɗaukakar kasancewarsa.

  12. Ishaya 3:9kusan 759 K.H.

    Fuskokinsu shaidu ne a kansu; suna nuna zunubinsu a fili kamar yadda Sodom ya yi; ba sa ma ɓoye shi. Kaitonsu! Sun jawo wa kansu masifa.

  13. Ishaya 3:10kusan 759 K.H.

    Ku faɗa wa masu adalci cewa kome zai zama musu da kyau, gama za su ji daɗin aikin da hannuwansu suka yi.

  14. Ishaya 3:11kusan 759 K.H.

    Kaiton masu mugunta! Masifa tana a kansu! Za a rama abin da hannuwansu suka yi.

  15. Ishaya 3:12kusan 759 K.H.

    Matasa suna zalunta mutanena, mata suna mulki a bisansu. Ya mutanena, jagorarinku suna ɓad da ku; suna karkatar da ku daga hanya.

  16. Ishaya 3:13kusan 759 K.H.

    Ubangiji ya ɗauki mazauninsa a cikin ɗakin shari’a; ya tashi don yă shari’anta mutane.

  17. Ishaya 3:14kusan 759 K.H.

    Ubangiji yana shari’a da dattawa da kuma shugabannin mutanensa, “Ku ne kuka lalace gonar inabina; ganimar talakawa suna a gidajenku.

  18. Ishaya 3:15kusan 759 K.H.

    Ina dalilin da kuke marmatsa mutanena kuna gurgurje fuskokin talakawa?” Ni Ubangiji Maɗaukaki na faɗa.

  19. Ishaya 3:16kusan 759 K.H.

    Ubangiji ya ce, “Matan Sihiyona suna da girman kai, suna tafiya da wuya a miƙe, da idanu masu yaudara, suna takawa ɗaya-ɗaya a hankali, da mundaye a ƙafafunsu, suna cas-cas.

  20. Ishaya 3:17kusan 759 K.H.

    Saboda haka Ubangiji zai kawo gyambuna a kawunan matan Sihiyona; Ubangiji zai sa a aske kawunansu, a bar su ƙwal.”

  21. Ishaya 3:18kusan 759 K.H.

    A wannan rana Ubangiji zai ƙwace abin da suke taƙama da shi, mundayensu, ɗankwalin kansu da abin wuyansu,

  22. Ishaya 3:19kusan 759 K.H.

    ’yan kunnensu, kwandagansu da lulluɓinsu,

  23. Ishaya 3:20kusan 759 K.H.

    kitsonsu, sarƙar da suke sa wa damatsansu da ɗamararsu, kwalabai turare da layu,

  24. Ishaya 3:21kusan 759 K.H.

    da ƙawanen da suka sa a yatsotsinsu da hancinsu,

  25. Ishaya 3:22kusan 759 K.H.

    tufafi masu kyau, da manyan rigunansu, da mayafansu, da jakar kuɗinsu