Skip to content

Ayoyin Littafi Mai Tsarki game da Jerusalem: Annual feasts kept at

17 ayoyi · 117 fannoni

Ayoyi game da Annual feasts kept at

  1. An gina Urushalima kamar birnin da aka yi a harhaɗe wuri guda.

  2. A can ne kabilu suke haurawa, kabilan Ubangiji, don su yabi sunan Ubangiji bisa ga farillan da aka ba wa Isra’ila.

  3. A can kursiyoyin shari’a yake tsaye, kursiyoyin gidan Dawuda.

  4. Bayan wannan, sai Yesu ya yi ta zagawa a cikin Galili, da ganga bai yarda yă je Yahudiya ba domin Yahudawa a can suna nema su kashe shi.

  5. Amma sa’ad da Bikin Tabanakul na Yahudawa ya yi kusa,

  6. sai ’yan’uwan Yesu suka ce masa, “Ya kamata ka bar nan ka tafi Yahudiya, don almajiranka su ga ayyukan banmamaki da kake yi.

  7. Ba wanda yake so a san shi da zai yi abu a ɓoye. Da yake kana yin waɗannan abubuwa, sai ka nuna kanka ga duniya.”

  8. Domin ko ’yan’uwansa ma ba su gaskata da shi ba.

  9. Saboda haka Yesu ya ce musu, “Lokacina bai yi ba tukuna; amma a gare ku kowane lokaci daidai ne.

  10. Duniya ba za tă iya ƙinku ba, amma ni take ƙi domin ina shaida cewa ayyukanta mugaye ne.

  11. Ku ku tafi Bikin, ba zan haura zuwa wannan Bikin ba yanzu, domin lokacina bai yi ba tukuna.”

  12. Da ya faɗa haka, sai ya dakata a Galili.

  13. Amma fa, bayan ’yan’uwansa suka tafi Bikin, shi ma ya tafi, ba a fili ba, amma a ɓoye.

  14. A Bikin kuwa, Yahudawa suka yi ta nemansa, suna cewa, “Ina mutumin yake?”

  15. A cikin taron kuwa aka yi ta raɗe-raɗe game da shi. Waɗansu suka ce, “Shi mutumin kirki ne.” Waɗansu kuwa suka ce, “A’a, ai, ruɗin mutane yake.”

  16. Amma ba wanda ya ce kome a fili game da shi don tsoron Yahudawa.

  17. Sai bayan da aka kai tsakiyar Bikin, sa’an nan Yesu ya haura zuwa filin haikali ya fara koyarwa.