circa 6 BC – AD 30
The Life of Jesus
The eternal Son of God enters history: born in Bethlehem, baptized in the Jordan, crucified at Golgotha, raised on the third day.
Ayoyi daga wannan lokacin
- Luka 23:10kusan 33 M.
Manyan firistoci da malaman dokoki suna tsaye a wurin, suna kawo zargi masu ƙarfi a kansa.
- Luka 23:11kusan 33 M.
Sai Hiridus da sojojinsa suka wulaƙanta shi, suka yi masa ba’a. Sa’an nan, suka sa masa babban riga, suka mai da shi wurin Bilatus.
- Luka 23:12kusan 33 M.
A ranar, Hiridus da Bilatus suka zama abokan juna, don tun dā ma, su abokan gāba ne.
- Luka 23:13kusan 33 M.
Bilatus ya tara manyan firistoci, da masu mulki, da mutane,
- Luka 23:14kusan 33 M.
ya ce musu, “Kun kawo mini wannan mutum, a matsayin wanda yana zuga mutane su yi tawaye. Na bincike shi a gabanku, ban ga a kan me kuka kawo kararsa ba.
- Luka 23:15kusan 33 M.
Haka ma Hiridus, shi ya sa ya dawo da shi nan wurinmu. Kamar yadda ku ma kun gani, ba abin da mutumin nan ya yi, da ya isa mutuwa.
- Luka 23:16kusan 33 M.
Saboda haka, zan yi masa bulala, in sāke shi.”
- Luka 23:17kusan 33 M.
(For of necessity he must release one unto them at the feast.)
- Luka 23:18kusan 33 M.
Suka yi ihu gaba ɗaya suka ce, “A yi gaba da wannan mutum! A sake mana Barabbas!”
- Luka 23:19kusan 33 M.
(Barabbas yana kurkuku saboda laifin tā da hankali a birnin, da kuma don kisankai.)
- Luka 23:20kusan 33 M.
Sai Bilatus ya sāke yin musu magana don yana so ya saki Yesu.
- Luka 23:21kusan 33 M.
Amma sai suka ci gaba da ihu, suna cewa, “A gicciye shi! A gicciye shi!”
- Luka 23:22kusan 33 M.
Ya sāke ce musu, sau na uku, “Don me? Wane laifi wannan mutum ya yi? Ni dai ban same shi da wani dalilin da ya isa a kashe shi ba. Saboda haka, zan sa a hore shi, sa’an nan in sāke shi.”
- Luka 23:23kusan 33 M.
Amma suna ihu, suna nacewa, suna cewa, dole a gicciye shi, har ihunsu ya rinjaye shi.
- Luka 23:24kusan 33 M.
Sai Bilatus ya biya bukatarsu da ya ji roƙonsu.
- Luka 23:25kusan 33 M.
Ya saki mutumin da aka jefa a kurkuku saboda tā da hankali, da kisankai, shi wanda suka roƙa. Sa’an nan ya ba da Yesu ga nufinsu.
- Luka 23:26kusan 33 M.
Sa’ad da suna tafiya da Yesu, sai wani da ake kira Siman, mutumin Sairin, yana zuwa daga ƙauye. Suka kama shi, suka aza masa gicciyen, suka tilasta shi ya ɗauki gicciyen, ya bi Yesu a baya.
- Luka 23:27kusan 33 M.
Mutane da yawa sosai suka bi shi, a cikinsu ma da mata waɗanda suka yi makoki da kuka dominsa.
- Luka 23:28kusan 33 M.
Yesu ya juya, ya ce musu, “’Yan matan Urushalima, kada ku yi kuka saboda ni, amma ku yi kuka saboda kanku, da kuma saboda ’ya’yanku.
- Luka 23:29kusan 33 M.
Gama lokaci yana zuwa da za ku ce, ‘Masu albarka ne bakararru, wato, mata marasa haihuwa, da mahaihuwar da ba su taɓa haihuwa ba, da kuma mama da ba su taɓa shayar da nono ba!’
- Luka 23:30kusan 33 M.
Sa’an nan “ ‘za su ce wa duwatsu, “Ku fāɗi a kanmu!” Za su ce wa tuddai kuma, “Ku rufe mu!” ’
- Luka 23:31kusan 33 M.
Gama in mutane suna yin waɗannan abubuwa a lokacin da itace na ɗanye, me zai faru in ya bushe?”
- Luka 23:32kusan 33 M.
Tare da shi akwai mutum biyu masu laifi, da aka tafi da su don a gicciye.
- Luka 23:33kusan 33 M.
Da suka isa wurin da ake kira “Ƙoƙon Kai,” nan suka gicciye shi, tare da masu laifin nan, ɗaya a hannun damansa, ɗayan kuma a hagunsa.
- Luka 23:34kusan 33 M.
Yesu ya ce, “Ya Uba ka yi musu gafara, don ba su san abin da suke yi ba.” Suka rarraba tufafinsa ta wurin jefa ƙuri’a.