circa 6 BC – AD 30
The Life of Jesus
The eternal Son of God enters history: born in Bethlehem, baptized in the Jordan, crucified at Golgotha, raised on the third day.
Ayoyi daga wannan lokacin
- Luka 22:56kusan 33 M.
Wata baiwa ta gan shi zaune kusa da wutar. Ta dube shi sosai sa’an nan, ta ce, “Ai, wannan mutum ma yana tare da shi.”
- Luka 22:57kusan 33 M.
Amma ya yi mūsu ya ce, “Mace, ban san shi ba!”
- Luka 22:58kusan 33 M.
Bayan ɗan lokaci kaɗan, wani dabam ya gan shi ya ce, “Kai ma ɗayansu ne.” Bitrus ya amsa ya ce, “Kai, ba na cikinsu!”
- Luka 22:59kusan 33 M.
Bayan kamar sa’a ɗaya, sai wani mutum ya ce, “Ba shakka, mutumin nan ma yana tare da shi, don shi mutumin Galili ne.”
- Luka 22:60kusan 33 M.
Bitrus ya amsa ya ce, “Kai, ban ma san abin da kake magana a kai ba!” Yana cikin magana, sai zakara ya yi cara.
- Luka 22:61kusan 33 M.
Ubangiji kuma ya juya ya kafa wa Bitrus ido. Sai Bitrus ya tuna da maganar da Ubangiji ya ce masa, “Kafin zakara ya yi cara yau, za ka yi mūsun sanina sau uku.”
- Luka 22:62kusan 33 M.
Sai ya fita waje, ya yi kuka mai zafi.
- Luka 22:63kusan 33 M.
Mutanen da suke gadin Yesu suka fara masa ba’a da dūka.
- Luka 22:64kusan 33 M.
Suka rufe masa idanu suna tambaya cewa, “Ka yi annabci! Wa ya mare ka?”
- Luka 22:65kusan 33 M.
Suka kuma yi masa waɗansu baƙaƙen maganganu masu yawa.
- Luka 22:66kusan 33 M.
Da gari ya waye, sai majalisar dattawa na mutane, da manyan firistoci, da malaman dokoki, suka taru wuri ɗaya. Sai aka kawo Yesu a gabansu.
- Luka 22:67kusan 33 M.
Suka ce, “Ka faɗa mana, ko kai ne Kiristi?” Yesu ya amsa ya ce, “Ko na gaya muku, ba za ku gaskata ni ba,
- Luka 22:68kusan 33 M.
in kuma na yi muku tambaya ba za ku iya ba ni amsa ba.
- Luka 22:69kusan 33 M.
Amma daga yanzu, Ɗan Mutum zai zauna a hannun dama na Allah Mai Iko.”
- Luka 22:70kusan 33 M.
Sai dukansu suka yi tambaya suka ce, “Wato, kai Ɗan Allah ke nan?” Ya amsa ya ce, “Kun faɗa daidai, ni ne.”
- Luka 22:71kusan 33 M.
Sai suka ce, “Wace shaida kuma muke nema? Ai, mun ji abin da ya ce da bakinsa.”
- Luka 23:1kusan 33 M.
Sai dukan majalisa suka tashi, suka kai shi gaban Bilatus.
- Luka 23:2kusan 33 M.
Suka fara zarginsa suna cewa, “Mun sami wannan mutum yana rikitar da al’ummarmu. Yana hana a biya haraji ga Kaisar. Yana kuma cewa, shi Kiristi ne, sarki kuma.”
- Luka 23:3kusan 33 M.
Sai Bilatus ya tambayi Yesu ya ce, “Kai ne sarkin Yahudawa?” Yesu ya amsa ya ce, “I, haka yake, kamar yadda ka faɗa.”
- Luka 23:4kusan 33 M.
Sai Bilatus ya sanar wa manyan firistoci da taron ya ce, “Ni fa, ban sami wani ainihin abin zargi game wannan mutum nan ba.”
- Luka 23:5kusan 33 M.
Amma suka nace, suna cewa, “Yana tā da hankulan mutane, ko’ina a Yahudiya da koyarwarsa. Ya fara daga Galili, ga shi har ya kai nan.”
- Luka 23:6kusan 33 M.
Da Bilatus ya ji haka, sai ya yi tambaya, “Ko shi mutumin Galili ne?”
- Luka 23:7kusan 33 M.
Da ya ji cewa, Yesu yana ƙarƙashin mulkin Hiridus ne, sai ya aika da shi zuwa wurin Hiridus, don a lokacin Hiridus yana Urushalima.
- Luka 23:8kusan 33 M.
Da Hiridus ya ga Yesu, sai ya yi murna ƙwarai, don tun dā ma yana marmari ya gan shi a kan abin da ya ji game da shi. Ya yi fata ya ga Yesu, yă kuma yi waɗansu ayyukan banmamaki.
- Luka 23:9kusan 33 M.
Ya yi masa tambayoyi masu yawa, amma Yesu bai ba shi ko amsa ba.