circa 6 BC – AD 30
The Life of Jesus
The eternal Son of God enters history: born in Bethlehem, baptized in the Jordan, crucified at Golgotha, raised on the third day.
Ayoyi daga wannan lokacin
- Luka 23:35kusan 33 M.
Mutanen suka tsaya suna kallo. Har masu mulki ma suka yi masa ba’a, suna cewa, “Ya ceci waɗansu, to, ya ceci kansa in shi ne Kiristi na Allah, Zaɓaɓɓe.”
- Luka 23:36kusan 33 M.
Sojoji su ma, suka zo suka yi masa ba’a. Suka miƙa masa ruwan tsami.
- Luka 23:37kusan 33 M.
Suka ce, “In kai ne sarkin Yahudawa, ka ceci kanka mana.”
- Luka 23:38kusan 33 M.
Bisa da shi kuma akwai rubutun da ya ce, Wannan shi ne Sarkin Yahudawa.
- Luka 23:39kusan 33 M.
Ɗaya daga cikin masu laifin da aka gicciye a wurin ya zazzage shi ya ce, “Shin, ba kai ne Kiristi ba? To, ka ceci kanka, ka kuma cece mu mana!”
- Luka 23:40kusan 33 M.
Amma ɗayan mai laifi ya kwaɓe shi ya ce, “Ba ka da tsoron Allah ne, wai saboda kana ƙarƙashin hukunci ɗaya tare da shi?
- Luka 23:41kusan 33 M.
Horonmu, daidai aka yi mana, sakamakon abin da muka yi ne. Amma wannan mutum, bai yi wani laifi ba.”
- Luka 23:42kusan 33 M.
Sai ya ce, “Yesu, ka tuna da ni sa’ad da ka shiga mulkinka.”
- Luka 23:43kusan 33 M.
Yesu ya amsa, ya ce masa, “Gaskiya nake faɗa maka, yau ɗin nan, za ka kasance tare da ni, a mulkina a sama.”
- Luka 23:44kusan 33 M.
Yanzu kuwa wajen sa’a ta shida ne, kuma duhu ya rufe ko’ina a ƙasar, har zuwa sa’a ta tara,
- Luka 23:45kusan 33 M.
domin rana ta daina haskakawa. Labulen da yake cikin haikali kuma ya yage kashi biyu.
- Luka 23:46kusan 33 M.
Yesu ya yi kira da babbar murya ya ce, “Ya Uba, na danƙa ruhuna a hannunka.” Da ya faɗi haka, sai ya ja numfashi na ƙarshe.
- Luka 23:47kusan 33 M.
Da jarumin ya ga abin da ya faru, sai ya yabi Allah ya ce, “Gaskiya, wannan mutum mai adalci ne.”
- Luka 23:48kusan 33 M.
Da dukan mutanen da suka taru, domin shaidar waɗannan abubuwa, suka ga abin da ya faru, sai suka buga ƙirjinsu suka tafi.
- Luka 23:49kusan 33 M.
Amma dukan mutanen da suka san Yesu, tare da mata da suka bi shi daga Galili, suka tsaya daga nesa suna kallon abubuwan nan.
- Luka 23:50kusan 33 M.
Akwai wani mutum mai suna Yusuf, ɗan Majalisa, wanda shi nagari ne, mai adalci,
- Luka 23:51kusan 33 M.
shi dā ma bai yarda da shawararsu, da kuma abin da suka yi ba. Shi daga Arimateya ne wani garin Yahudiya. Yana kuma jiran zuwa mulkin Allah.
- Luka 23:52kusan 33 M.
Sai ya je wurin Bilatus ya roƙa a ba shi jikin Yesu.
- Luka 23:53kusan 33 M.
Sai ya saukar da jikin, ya nannaɗe shi a cikin zanen lilin, ya sa shi a wani kabari da aka fafe a cikin dutse, wadda ba a taɓa sa kowa ba.
- Luka 23:54kusan 33 M.
An yi haka ne a Ranar Shirye-shirye, ranar Asabbaci kuma yana dab da farawa.
- Luka 23:55kusan 33 M.
Matan da suka zo tare da Yesu, daga Galili suka bi Yusuf suka ga kabarin, da kuma yadda aka ajiye jikin.
- Luka 23:56kusan 33 M.
Sa’an nan, suka koma gida, suka shirya kayan ƙanshi da turare. Amma suka huta a ranar Asabbaci don kiyaye doka.
- Luka 24:1kusan 33 M.
Da sassafe a ranar farko ta mako, matan suka je kabarin, da kayan ƙanshin da suka shirya.
- Luka 24:2kusan 33 M.
Suka iske an riga an gungurar da dutsen daga bakin kabarin.
- Luka 24:3kusan 33 M.
Amma da suka shiga ciki, ba su iske jikin Ubangiji Yesu ba.