Tsallake zuwa abun ciki

circa 6 BC – AD 30

The Life of Jesus

The eternal Son of God enters history: born in Bethlehem, baptized in the Jordan, crucified at Golgotha, raised on the third day.

3,779 ayoyi · 4 littattafai da aka rufe

Ayoyi daga wannan lokacin

Tace bisa littafi
  1. Luka 24:29kusan 33 M.

    Amma suka matsa masa suka ce, “Sauka wurinmu, don dare ya kusa, rana ta kusa fāɗuwa.” Sai ya sauka wurinsu.

  2. Luka 24:30kusan 33 M.

    Da ya zauna a tebur tare da su, sai ya ɗauki burodi, ya yi godiya, ya kakkarya ya fara ba su.

  3. Luka 24:31kusan 33 M.

    Sa’an nan idanunsu suka buɗe, suka gane shi. Sai ya ɓace musu.

  4. Luka 24:32kusan 33 M.

    Suka tambayi juna, “Ashe, shi ya sa zukatanmu suka kuna a cikinmu, sa’ad da yake magana da mu a hanya, yana bayyana mana Nassi.”

  5. Luka 24:33kusan 33 M.

    Suka tashi nan da nan suka koma Urushalima. A can suka sami Sha Ɗayan nan da waɗanda suke tare da su a wuri ɗaya,

  6. Luka 24:34kusan 33 M.

    suna cewa, “Gaskiya ne! Ubangiji ya tashi, ya kuma bayyana ga Siman”

  7. Luka 24:35kusan 33 M.

    Sai su biyun nan suka ba da labarin abin da ya faru a hanya, da kuma yadda suka gane Yesu yayinda ya kakkarya burodin.

  8. Luka 24:36kusan 33 M.

    Suna cikin wannan zance, sai ga Yesu da kansa tsaye a tsakiyarsu. Sai ya ce musu, “Salama a gare ku!”

  9. Luka 24:37kusan 33 M.

    Suka firgita, suka tsorota, suna tsammani fatalwa ce suka gani.

  10. Luka 24:38kusan 33 M.

    Sai ya ce musu, “Don me kuke damuwa, kuke kuma shakka a zuciyarku?

  11. Luka 24:39kusan 33 M.

    Ku duba hannuwana da ƙafafuna. Ai, ni ne da kaina! Ku taɓa ni ku ji, ai, fatalwa ba ta da nama da ƙashi, yadda kuke gani nake da su.”

  12. Luka 24:40kusan 33 M.

    Da ya faɗi haka, sai ya nuna musu hannuwansa da ƙafafunsa.

  13. Luka 24:41kusan 33 M.

    Kuma har yanzu, suna cikin rashin gaskatawa, saboda murna da mamaki, sai ya tambaye su, “Kuna da abinci a nan?”

  14. Luka 24:42kusan 33 M.

    Suka ba shi ɗan gasasshen kifi,

  15. Luka 24:43kusan 33 M.

    ya karɓa ya ci a gabansu.

  16. Luka 24:44kusan 33 M.

    Ya ce musu, “Wannan shi ne abin da na gaya muku tun ina tare da ku cewa, dole a cika kome da aka rubuta game da ni, a cikin Dokar Musa, da Annabawa, da kuma Zabura.”

  17. Luka 24:45kusan 33 M.

    Sai ya wayar da tunaninsu don su fahimci Nassi.

  18. Luka 24:46kusan 33 M.

    Ya ce musu, “Wannan shi ne abin da aka rubuta, cewa dole Kiristi yă sha wahala, a rana ta uku kuma yă tashi daga matattu.

  19. Luka 24:47kusan 33 M.

    Kuma a cikin sunansa za a yi wa’azin tuba da gafarar zunubai, ga dukan ƙasashe. Za a kuwa fara daga Urushalima.

  20. Luka 24:48kusan 33 M.

    Ku ne shaidun waɗannan abubuwa.

  21. Luka 24:49kusan 33 M.

    Zan aika muku da abin da Ubana ya yi alkawari. Amma ku dakata a birnin tukuna, sai an rufe ku da iko daga sama.”

  22. Luka 24:50kusan 33 M.

    Bayan ya kai su waje kusa da Betani, sai ya ɗaga hannuwansa ya sa musu albarka.

  23. Luka 24:51kusan 33 M.

    Yana cikin sa musu albarka, sai ya rabu da su. Aka ɗauke shi zuwa cikin sama.

  24. Luka 24:52kusan 33 M.

    Sai suka yi masa sujada, suka koma Urushalima cike da murna sosai.

  25. Luka 24:53kusan 33 M.

    Sai suka ci gaba da zama a cikin haikalin, suna yabon Allah.