Tsallake zuwa abun ciki

circa 6 BC – AD 30

The Life of Jesus

The eternal Son of God enters history: born in Bethlehem, baptized in the Jordan, crucified at Golgotha, raised on the third day.

3,779 ayoyi · 4 littattafai da aka rufe

Ayoyi daga wannan lokacin

Tace bisa littafi
  1. Luka 24:4kusan 33 M.

    Yayinda suna cikin tunani a kan wannan, nan take, ga waɗansu mutum biyu tsaye kusa da su, sanye da kaya masu ƙyalli, kamar walƙiya.

  2. Luka 24:5kusan 33 M.

    A cikin tsoro, matan suka fāɗi da fuskokinsu a ƙasa, amma mutanen suka ce musu, “Me ya sa kuke neman mai rai a cikin matattu?

  3. Luka 24:6kusan 33 M.

    Ba ya nan, ya tashi! Ku tuna yadda ya gaya muku tun yana tare da ku a Galili cewa,

  4. Luka 24:7kusan 33 M.

    ‘Dole a ba da Ɗan Mutum ga hannun masu zunubi, a kuma gicciye shi, a rana ta uku kuma a tashe shi.’ ”

  5. Luka 24:8kusan 33 M.

    Sai suka tuna da maganarsa.

  6. Luka 24:9kusan 33 M.

    Da suka dawo daga kabarin, sai suka faɗa wa Sha Ɗayan nan da sauransu, dukan waɗannan abubuwa.

  7. Luka 24:10kusan 33 M.

    Matan da suka gaya wa manzannin waɗannan abubuwa su ne, Maryamu Magdalin, da Yowanna, da Maryamu uwar Yaƙub, da waɗansu da suke tare da su.

  8. Luka 24:11kusan 33 M.

    Amma ba su gaskata matan ba, domin sun ɗauki kalmominsu wani zancen banza ne.

  9. Luka 24:12kusan 33 M.

    Duk da haka, Bitrus ya tashi a guje zuwa kabarin. Da ya sunkuya, sai ya ga ƙyallayen lilin kaɗai a kwance. Sai ya koma yana tunani a ransa, a kan abin da ya faru.

  10. Luka 24:13kusan 33 M.

    A wannan rana kuma, biyu daga cikinsu suna tafiya zuwa wani ƙauye, da ake kira Emmawus, da suke kusan mil bakwai daga Urushalima.

  11. Luka 24:14kusan 33 M.

    Suna magana da juna a kan dukan abubuwan da suka faru.

  12. Luka 24:15kusan 33 M.

    Da suna magana, kuma suna tattauna waɗannan abubuwa da junansu, sai Yesu da kansa ya zo yana tafiya tare da su.

  13. Luka 24:16kusan 33 M.

    Amma ba a ba su ikon gane shi ba.

  14. Luka 24:17kusan 33 M.

    Sai ya tambaye, su ya ce, “Mene ne kuke tattaunawa da juna a cikin tafiyarku?” Suka tsaya shiru, da damuwa a fuskarsu.

  15. Luka 24:18kusan 33 M.

    Ɗaya daga cikinsu, mai suna Kiliyobas, ya tambaye shi ya ce, “Ashe, kai baƙo ne a Urushalima, da ba ka san abubuwan da suka faru a can, a cikin kwanakin nan ba?”

  16. Luka 24:19kusan 33 M.

    Sai ya yi tambaya, “Waɗanne abubuwa?” Suka amsa suka ce, “Game da Yesu Banazare. Shi annabi ne, mai iko ne kuma cikin ayyukansa da maganarsa, a gaban Allah da kuma dukan mutane.

  17. Luka 24:20kusan 33 M.

    Manyan firistoci da masu mulkinmu sun ba da shi a yi masa hukuncin mutuwa, suka kuwa gicciye shi.

  18. Luka 24:21kusan 33 M.

    Amma da, muna sa zuciya cewa, shi ne wanda zai fanshi Isra’ila. Bugu da ƙari kuma yau kwana uku ke nan tun da wannan abin ya faru.

  19. Luka 24:22kusan 33 M.

    Har wa yau, waɗansu daga cikin matanmu sun ba mu mamaki. Sun je kabarin da sassafen nan,

  20. Luka 24:23kusan 33 M.

    amma ba su sami jikinsa ba. Sun dawo sun faɗa mana cewa, sun ga wahayi na mala’iku, da suka ce yana da rai.

  21. Luka 24:24kusan 33 M.

    Sa’an nan, waɗansu abokanmu suka je kabarin, suka kuma tarar da kome kamar yadda matan suka faɗa, amma shi, ba su gan shi ba.”

  22. Luka 24:25kusan 33 M.

    Sai ya ce musu, “Ashe, ku marasa azanci ne, masu nauyin zuciyar gaskata, da dukan abin da annabawa suka faɗa!

  23. Luka 24:26kusan 33 M.

    Ai, dole Kiristi yă sha waɗannan wahalolin, kafin yă shiga ɗaukakarsa.

  24. Luka 24:27kusan 33 M.

    Sai ya fara bayyana musu daga Musa da dukan Annabawa, abin da dukan Nassi ya faɗa a kansa.”

  25. Luka 24:28kusan 33 M.

    Da suka yi kusa da ƙauyen da za su, sai Yesu ya yi kamar zai ci gaba.