circa 6 BC – AD 30
The Life of Jesus
The eternal Son of God enters history: born in Bethlehem, baptized in the Jordan, crucified at Golgotha, raised on the third day.
Ayoyi daga wannan lokacin
- Luka 22:6kusan 33 M.
Ya ko yarda, ya fara neman zarafin da zai ba da Yesu a gare su, sa’ad da taro ba sa nan tare da shi.
- Luka 22:7kusan 33 M.
Sai ranar Bikin Burodi Marar Yisti ta kewayo, wato, ranar hadayar ɗan ragon kafara na Bikin Ƙetarewa.
- Luka 22:8kusan 33 M.
Sai Yesu ya aiki Bitrus da Yohanna, ya ce musu, “Ku je ku yi shirye-shiryen Bikin Ƙetarewar da za mu ci.”
- Luka 22:9kusan 33 M.
Suka tambaye shi suka ce, “Ina kake so mu je mu yi shirin?”
- Luka 22:10kusan 33 M.
Ya amsa ya ce, “Sa’ad da kuka shiga cikin gari, za ku sadu da wani mutum yana ɗauke da tulun ruwa. Ku bi shi zuwa gidan da zai shiga.
- Luka 22:11kusan 33 M.
Ku ce wa maigidan, Malam ya aike mu mu ce maka, ‘Ina ɗakin baƙi, inda ni da almajiraina za mu ci abincin Bikin Ƙetarewa?’
- Luka 22:12kusan 33 M.
Zai nuna muku wani babban ɗakin sama a shirye. Nan za ku yi shirin.”
- Luka 22:13kusan 33 M.
Sai suka tafi, suka kuma iske kome kamar yadda Yesu ya faɗa musu. Sai suka shirya Bikin Ƙetarewa.
- Luka 22:14kusan 33 M.
Da lokaci ya yi, sai Yesu ya zauna tare da manzanninsa don cin abinci.
- Luka 22:15kusan 33 M.
Sai ya ce musu, “Na yi marmari ƙwarai don in ci wannan Bikin Ƙetarewa tare da ku, kafin in sha wahala.
- Luka 22:16kusan 33 M.
Ina dai gaya muku, ba zan ƙara cinsa ba, sai ya sami cika a mulkin Allah.”
- Luka 22:17kusan 33 M.
Bayan ya ɗauki kwaf ruwan inabi, ya yi godiya, sai ya ce, “Ku karɓa, ku rarraba wa junanku.
- Luka 22:18kusan 33 M.
Ina dai gaya muku, ba zan ƙara sha daga ’ya’yan inabi ba, sai mulkin Allah ya zo.”
- Luka 22:19kusan 33 M.
Sai ya ɗauki burodi ya yi godiya, ya kakkarya ya ba su, da cewa, “Wannan jikina ne, da aka bayar dominku. Ku riƙa yin haka don tunawa da ni.”
- Luka 22:20kusan 33 M.
Haka kuma, bayan abincin, ya ɗauki kwaf ruwan inabi ya ce, “Wannan kwaf ruwan inabi shi ne, na sabon alkawari cikin jinina, da aka zubar dominku.
- Luka 22:21kusan 33 M.
Amma hannun wanda zai ci amanata, yana cin abincin tare da ni.
- Luka 22:22kusan 33 M.
Ɗan Mutum zai mutu kamar yadda aka ƙaddara, amma kaiton mutumin da zai bashe shi.”
- Luka 22:23kusan 33 M.
Sai suka fara tambayar junansu, ko wane ne a cikinsu zai yi wannan.
- Luka 22:24kusan 33 M.
Gardama ta tashi a tsakaninsu, a kan ko wane ne a cikinsu ya fi girma.
- Luka 22:25kusan 33 M.
Yesu ya ce musu, “Sarakunan Al’ummai suna nuna iko a kan mutanensu, kuma waɗanda suke nuna iko a kansu, suna kiran kansu Masu Taimakon mutane.
- Luka 22:26kusan 33 M.
Amma ku, kada ku zama haka. A maimakon haka, sai dai wanda ya fi girma a cikinku, ya zama kamar wanda ya fi ƙanƙanta, wanda kuma ke mulki, ya zama kamar mai hidima.
- Luka 22:27kusan 33 M.
Wane ne ya fi girma? Wanda yake zaune a tebur ne, ko kuma shi da yake yin hidima? Ashe, ba wanda yake zaune a tebur ba ne? Amma ga ni, ni mai yin hidima ne a cikinku.
- Luka 22:28kusan 33 M.
Ku ne kuka tsaya tare da ni a gwaje-gwajen da na sha.
- Luka 22:29kusan 33 M.
Daidai kamar yadda Ubana ya ba ni mulki, haka ni ma nake ba ku.
- Luka 22:30kusan 33 M.
Saboda ku ci, ku sha a teburina a cikin mulkina. Kuma ku zauna a kan gadon sarauta, ku yi wa kabilu goma sha biyu na Isra’ila shari’a.