Tsallake zuwa abun ciki

circa 6 BC – AD 30

The Life of Jesus

The eternal Son of God enters history: born in Bethlehem, baptized in the Jordan, crucified at Golgotha, raised on the third day.

3,779 ayoyi · 4 littattafai da aka rufe

Ayoyi daga wannan lokacin

Tace bisa littafi
  1. Luka 20:41kusan 33 M.

    Sai Yesu ya ce musu, “Yaya suke cewa, ‘Kiristi ɗan Dawuda ne?’

  2. Luka 20:42kusan 33 M.

    Dawuda da kansa ya faɗa a cikin Zabura, “ ‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana,

  3. Luka 20:43kusan 33 M.

    sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka.” ’

  4. Luka 20:44kusan 33 M.

    Dawuda ya kira shi ‘Ubangiji.’ Ta, yaya zai zama ɗansa?”

  5. Luka 20:45kusan 33 M.

    Yayinda dukan mutane suna cikin sauraronsa, sai Yesu ya ce wa almajiransa,

  6. Luka 20:46kusan 33 M.

    “Ku yi hankali da malaman dokoki. Sukan so sa manyan riguna suna zaga, suna sha’awan karɓan gaisuwa a wuraren kasuwanci, da kuma wuraren zama mafi daraja a majami’u, da wuraren bangirma a bukukkuwa.

  7. Luka 20:47kusan 33 M.

    Suna mamaye gidajen gwauraye, kuma don burga, suna dogayen addu’o’i. Ga irin waɗannan mutane, za a yi musu hukunci mai tsanani sosai.”

  8. Luka 21:1kusan 33 M.

    Da Yesu ya ɗaga ido, sai ya ga waɗansu masu arziki suna sa baikonsu a ma’ajin haikalin.

  9. Luka 21:2kusan 33 M.

    Ya kuma ga wata gwauruwa matalauciya, ta saka anini biyu.

  10. Luka 21:3kusan 33 M.

    Sai ya ce, “Gaskiya ina faɗa muku, wacce nan gwauruwa matalauciya ta sa fiye da dukan sauran.

  11. Luka 21:4kusan 33 M.

    Dukan mutanen nan sun ba da baikonsu daga cikin arzikinsu ne, amma ita daga cikin talaucinta, ta saka duk abin da take da shi na rayuwa.”

  12. Luka 21:5kusan 33 M.

    Waɗansu daga cikin almajiransa, suka fara magana a kan yadda aka yi wa haikalin ado da duwatsu masu kyau, da kuma kyautai da aka keɓe wa Allah. Amma Yesu ya ce,

  13. Luka 21:6kusan 33 M.

    “Wannan abin da kuke kallo a nan, lokaci yana zuwa da ba za a bar wani dutse a kan wani dutse ba. Kowannensu, za a rushe shi.”

  14. Luka 21:7kusan 33 M.

    Suka tambaye shi suka ce, “Malam, yaushe waɗannan za su faru? Kuma wace alama za tă nuna cewa suna dab da faruwa?”

  15. Luka 21:8kusan 33 M.

    Ya amsa ya ce, “Ku lura, kada ku kuma a ruɗe ku. Gama da yawa za su zo a cikin sunana, suna cewa, ‘Ai, ni ne shi,’ da kuma, ‘Lokaci ya yi kusa.’ Kada ku bi su.

  16. Luka 21:9kusan 33 M.

    Sa’ad da kuka ji labarin yaƙe-yaƙe, da juye juyen mulki, kada ku tsorota. Dole ne waɗannan abubuwa su fara faruwa, amma ƙarshen ba zai zo nan da nan ba.”

  17. Luka 21:10kusan 33 M.

    Sai ya ce musu, “Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki zai tasar wa mulki.

  18. Luka 21:11kusan 33 M.

    Za a yi manyan girgizar ƙasa, da yunwa, da annoba a wurare dabam-dabam, da kuma abubuwa masu bantsoro, da manyan alamu daga sama.

  19. Luka 21:12kusan 33 M.

    “Amma kafin duk abubuwa nan, za a kama ku a tsananta muku. Za a kai ku majami’u, da kurkuku. Za a kuma kai ku gaban sarakuna da gwamnoni, kuma dukan waɗannan saboda sunana.

  20. Luka 21:13kusan 33 M.

    Wannan zai sa ku zama shaidu a gare su.

  21. Luka 21:14kusan 33 M.

    Amma ku yi ƙuduri, wato, ku shirya zuciyarku, a kan ba za ku damu ba kafin lokacin, game da yadda za ku kāre kanku.

  22. Luka 21:15kusan 33 M.

    Gama zan ba ku kalmomi, da hikima waɗanda ba ko ɗaya daga cikin maƙiyanku, za su iya tsayayya da ku, ko su ƙaryata.

  23. Luka 21:16kusan 33 M.

    Har iyayenku, da ’yan’uwanku maza, da danginku, da abokanku ma, duk za su bashe ku, su kuma kashe waɗansunku.

  24. Luka 21:17kusan 33 M.

    Duk mutane za su ƙi ku saboda ni.

  25. Luka 21:18kusan 33 M.

    Amma ko gashi ɗaya na kanku, ba zai hallaka ba.