circa 6 BC – AD 30
The Life of Jesus
The eternal Son of God enters history: born in Bethlehem, baptized in the Jordan, crucified at Golgotha, raised on the third day.
Ayoyi daga wannan lokacin
- Luka 19:39kusan 33 M.
Sai waɗansu Farisiyawa a cikin taron suka ce wa Yesu, “Malam, ka kwaɓi almajiranka!”
- Luka 19:40kusan 33 M.
Ya amsa ya ce, “Ina gaya muku, ko da sun yi shiru, duwatsu za su fara kirari.”
- Luka 19:41kusan 33 M.
Da ya yi kusa da Urushalima, ya kuma ga birnin, sai ya yi kuka a kanta,
- Luka 19:42kusan 33 M.
kuma ya ce, “In ke, ko ke ɗin ma, dā ma kin san abin da zai kawo miki salama a wannan rana, amma yanzu an ɓoye shi daga idanunki.
- Luka 19:43kusan 33 M.
Ranakun za su auko miki, a lokacin da abokan gābanki za su gina bango gāba da ke, su kuma kewaye inda kike, za su kuma tsare kowane gefenki, su sa ke a tsakiya.
- Luka 19:44kusan 33 M.
Za su fyaɗa ke a ƙasa, ke da ’ya’yan da suke cikin katanganki. Ba za su bar wani dutse a kan wani ba, saboda ba ki gane da lokacin da Allah zai ziyarce ki ba.”
- Luka 19:45kusan 33 M.
Sai ya shiga filin haikali, ya fara korar masu sayar da kaya.
- Luka 19:46kusan 33 M.
Ya ce musu, “A rubuce, yake cewa, ‘Gidana, zai zama gidan addu’a,’amma ga shi kun mai da shi ‘kogon ’yan fashi.’ ”
- Luka 19:47kusan 33 M.
Kowace rana, ya yi ta koyarwa a haikalin. Amma manyan firistoci, da malaman dokoki, da shugabannin mutane, suna ƙoƙarin kashe shi.
- Luka 19:48kusan 33 M.
Amma ba su sami hanyar yin haka ba, domin kalmominsa sun kama hankalin dukan mutanen.
- Luka 20:1kusan 33 M.
Wata rana da Yesu yana koyar da mutane, yana musu wa’azin bishara a filin haikalin, sai manyan firistoci da malaman dokoki, tare da dattawan suka zo wurinsa.
- Luka 20:2kusan 33 M.
Suka ce masa, “Gaya mana, da wane iko kake yin waɗannan abubuwa. Wa ya ba ka wannan ikon?”
- Luka 20:3kusan 33 M.
Ya amsa ya ce, “Ni ma zan yi muku wata tambaya. Ku faɗa mini,
- Luka 20:4kusan 33 M.
baftismar Yohanna, daga sama ne ta fito, ko kuwa daga wurin mutane ne?”
- Luka 20:5kusan 33 M.
Sai suka yi shawara da junansu, suka ce, “In muka ce, ‘Daga sama ne,’ zai tambaya, ‘To, don me ba ku gaskata shi ba?’
- Luka 20:6kusan 33 M.
Amma in kuma muka ce, ‘Daga mutane ne,’ dukan mutanen za su jajjefe mu da duwatsu, domin sun tabbata cewa, Yohanna annabi ne.”
- Luka 20:7kusan 33 M.
Don haka, sai suka amsa cewa, “Ba mu san inda ta fito ba.”
- Luka 20:8kusan 33 M.
Yesu ya ce, “To, ni ma ba zan gaya muku, ko da wane iko ne, nake yin waɗannan abubuwa ba.”
- Luka 20:9kusan 33 M.
Sai ya ci gaba da gaya wa mutanen wannan misali ya ce, “Wani mutum ya yi gonar inabi, sai ya ba da hayarta ga waɗansu manoma, sa’an nan ya yi wata doguwar tafiya.
- Luka 20:10kusan 33 M.
A lokacin girbi, sai ya aiki bawa zuwa wurin masu hayan, don su ba shi daga cikin ’ya’yan inabin. Amma ’yan hayan suka yi wa bawan nan dūka, suka kore shi hannu wofi.
- Luka 20:11kusan 33 M.
Ya sāke aikan wani bawa, shi ma suka yi masa dūka, suka kunyata shi, suka kuma kore shi hannu wofi.
- Luka 20:12kusan 33 M.
Har yanzu, ya sāke aikan na uku, amma suka ji masa rauni, suka jefar da shi waje.
- Luka 20:13kusan 33 M.
“Sai mai gonar inabin ya ce, ‘Me zan yi? Zan aiki ɗana da nake ƙauna, wataƙila za su girmama shi.’
- Luka 20:14kusan 33 M.
“Amma da ’yan hayan suka gan shi, sai suka tattauna zancen, suka ce, ‘Wannan shi ne magājin, mu kashe shi sa’an nan gādon zai zama namu!’
- Luka 20:15kusan 33 M.
Sai suka fitar da shi waje, suka kashe shi. “To, me mai gonar inabin zai yi da su?