circa 6 BC – AD 30
The Life of Jesus
The eternal Son of God enters history: born in Bethlehem, baptized in the Jordan, crucified at Golgotha, raised on the third day.
Ayoyi daga wannan lokacin
- Luka 19:14kusan 33 M.
“Amma talakawansa suka ƙi shi, sai suka aikar da wakilai bayansa, domin su ce, ‘Ba mu son wannan mutum ya zama sarkinmu.’
- Luka 19:15kusan 33 M.
“Duk da haka, aka naɗa shi sarki, sa’an nan ya dawo gida. Sai ya aika aka kira bayin da ya ba su kuɗin, don yă san ribar da suka samu.
- Luka 19:16kusan 33 M.
“Na fari ya zo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, minarka ya sami ribar goma.’
- Luka 19:17kusan 33 M.
“Maigidan ya amsa ya ce, ‘Madalla, bawana mai kirki! Tun da ka yi aminci a kan abu ƙanƙani, ka yi riƙon birane goma.’
- Luka 19:18kusan 33 M.
“Na biyun ya zo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, minarka ya sami ribar biyar.’
- Luka 19:19kusan 33 M.
“Maigidansa ya ce, ‘Kai ka yi riƙon birane biyar.’
- Luka 19:20kusan 33 M.
“Sai wani bawan ya zo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, ga minarka. Na ɓoye shi a wani ɗan tsumma.
- Luka 19:21kusan 33 M.
Na ji tsoronka, don kai mai wuyan sha’ani ne. Kakan ɗauki abin da ba ka ajiye ba, kakan kuma yi girbin abin da ba ka shuka ba.’
- Luka 19:22kusan 33 M.
“Sai maigidansa, ya amsa ya ce, ‘Zan hukunta ka a kan kalmominka, kai mugun bawa! Ashe, ka san cewa ni mai wuyan sha’ani ne, nakan ɗauka abin da ban ajiye ba, ina kuma girbin abin da ban shuka ba?
- Luka 19:23kusan 33 M.
Don me ba ka sa kuɗina a wajen ajiya, don in na dawo, in sami riba a kai ba?’
- Luka 19:24kusan 33 M.
“Sai ya ce wa waɗanda suke tsaye a wajen, ‘Ku karɓi minarsa ku ba wa wanda yake da mina goma.’
- Luka 19:25kusan 33 M.
“Suka ce, ‘Ranka yă daɗe, ai, yana da guda goma ko!’
- Luka 19:26kusan 33 M.
“Ya amsa ya ce, ‘Ina gaya muku, duk wanda yake da abu, za a ƙara masa. Amma wanda ba shi da shi kuwa, ko abin da yake da shi ma, za a karɓe.
- Luka 19:27kusan 33 M.
Amma waɗannan abokan gābana, waɗanda ba su so in zama sarkinsu ba, ku kawo su nan, ku karkashe su, a gabana.’ ”
- Luka 19:28kusan 33 M.
Bayan Yesu ya yi wannan magana, sai ya yi gaba zuwa Urushalima.
- Luka 19:29kusan 33 M.
Da ya kai kusa da Betfaji da Betani, a tudun da ake kira Dutsen Zaitun, sai ya aiki almajiransa guda biyu, ya ce musu,
- Luka 19:30kusan 33 M.
“Ku je ƙauyen da yake gaba da ku. Da kuna shiga, za ku tarar da wani ɗan jaki, wadda ba wanda ya taɓa hawa, a daure a wurin. Ku kunce shi ku kawo nan.
- Luka 19:31kusan 33 M.
In wani ya tambaye ku, ‘Don me kuke kunce shi?’ Ku ce masa, ‘Ubangiji yana bukatarsa.’ ”
- Luka 19:32kusan 33 M.
Waɗanda aka aika su yi gaba suka tafi, suka kuwa tarar kamar yadda ya gaya musu.
- Luka 19:33kusan 33 M.
Suna cikin kunce ɗan jakin, sai masu ɗan jakin suka ce musu, “Don me kuke kunce shi?”
- Luka 19:34kusan 33 M.
Suka amsa suka ce, “Ubangiji ne na bukatarsa.”
- Luka 19:35kusan 33 M.
Suka kawo shi wurin Yesu. Suka sa rigunarsu a kan ɗan jakin, sa’an nan suka sa Yesu a kai.
- Luka 19:36kusan 33 M.
Yana cikin tafiya, sai mutane suka shimfiɗa rigunarsu a kan hanya.
- Luka 19:37kusan 33 M.
Da ya yi kusa da wurin da hanyar ta gangara zuwa Dutsen Zaitun, sai dukan taron almajirai suka fara yabon Allah, da muryoyi masu ƙarfi, da murna, saboda dukan ayyukan banmamaki da suka gani. Suna cewa,
- Luka 19:38kusan 33 M.
“Mai albarka ne sarki wanda yake zuwa cikin sunan Ubangiji!” “Salama ta kasance a sama, da ɗaukaka kuma a can cikin sama!”