circa 6 BC – AD 30
The Life of Jesus
The eternal Son of God enters history: born in Bethlehem, baptized in the Jordan, crucified at Golgotha, raised on the third day.
Ayoyi daga wannan lokacin
- Luka 20:16kusan 33 M.
Zai zo ya karkashe masu hayan nan, ya ba wa waɗansu gonar inabin.” Da mutanen suka ji wannan, sai suka ce, “Allah ya sawwaƙa!”
- Luka 20:17kusan 33 M.
Yesu ya zura musu ido ya ce, “To, mene ne ma’anar abin da aka rubuta cewa, “ ‘Dutsen da magina suka ƙi, shi ne kuwa ya zama dutsen kan ginin’
- Luka 20:18kusan 33 M.
Duk wanda ya fāɗi a kan dutsen nan, zai kakkarye. Kuma in dutsen nan ya fāɗi a kan wani, zai murƙushe shi.”
- Luka 20:19kusan 33 M.
Malaman dokoki da manyan firistoci, suka nemi hanyar kama shi nan da nan, domin sun san cewa, ya yi wannan misali a kansu ne, amma suna jin tsoron mutane.
- Luka 20:20kusan 33 M.
Sai suka sa masa ido, suka aiki ’yan leƙen asiri, waɗanda suka nuna kamar su masu gaskiya ne, suna nufin su kama shi game da abin da zai faɗa, domin su ba da shi ga gwamna mai mulki, da mai iko.
- Luka 20:21kusan 33 M.
Sai ’yan leƙen asirin suka tambaye shi, suka ce, “Malam, mun sani kana faɗin, kuma kana koyar da abin da yake daidai, ba ka kuma nuna bambanci, amma kana koyar da hanyar Allah bisa ga gaskiya.
- Luka 20:22kusan 33 M.
Daidai ne mu biya haraji ga Kaisar, ko babu?”
- Luka 20:23kusan 33 M.
Ya gane makircinsu, sai ya ce musu,
- Luka 20:24kusan 33 M.
“Nuna mini dinari. Hoton wane ne, kuma rubutun wane ne a kai?” Suka amsa, “Na Kaisar.”
- Luka 20:25kusan 33 M.
Sai ya ce musu, “Ku ba wa Kaisar abin da yake na Kaisar, ku kuma ba wa Allah abin da yake na Allah.”
- Luka 20:26kusan 33 M.
Ba su iya kama shi a kan abin da ya faɗa a fili ba. Amsarsa ya ba su mamaki, shi ya sa suka yi shiru.
- Luka 20:27kusan 33 M.
Waɗansu Sadukiyawa da suke cewa, ba tashin matattu, suka zo wurin Yesu da tambaya cewa,
- Luka 20:28kusan 33 M.
“Malam, Musa ya rubuta mana cewa, ‘In ɗan’uwan wani mutum ya mutu, ya bar mata amma ba ’ya’ya, dole mutumin ya aure gwauruwar, ya samo wa ɗan’uwansa ’ya’ya.’
- Luka 20:29kusan 33 M.
To, an yi waɗansu ’yan’uwa bakwai. Na fari ya auri wata mace, ya mutu ba ’ya’ya.
- Luka 20:30kusan 33 M.
Na biyun,
- Luka 20:31kusan 33 M.
da na ukun suka aure ta. Haka nan dukansu bakwai suka mutu babu ’ya’ya.
- Luka 20:32kusan 33 M.
A ƙarshe, ita macen ma ta mutu.
- Luka 20:33kusan 33 M.
Shin, a tashin matattu, matar wa za tă zama? Tun da su bakwan nan, sun aure ta.”
- Luka 20:34kusan 33 M.
Yesu ya amsa ya ce, “Mutanen zamanin nan suna aure, suna kuma ba da aure,
- Luka 20:35kusan 33 M.
amma su waɗanda aka ga sun cancantar kasancewa a zamanin can, da kuma na tashin matattu, ba za su yi aure, ko su ba da aure ba.
- Luka 20:36kusan 33 M.
Kuma ba za su sāke mutuwa ba, gama su kamar mala’iku ne. Su ’ya’yan Allah ne, tun da su ’ya’yan tashin matattu ne.
- Luka 20:37kusan 33 M.
Amma bisa ga labari na bishiya nan, mai cin wuta da Musa ya gani a jeji, ko Musa ma, ya nuna cewa, matattu suna tashi. Gama ya kira Ubangiji, ‘Allah na Ibrahim, da Allah na Ishaku, da kuma Allah na Yaƙub.’
- Luka 20:38kusan 33 M.
Shi ba Allah na matattu ba ne, amma na masu rai ne, gama a gare shi, duka na da rai.”
- Luka 20:39kusan 33 M.
Sai waɗansu malaman dokoki suka amsa suka ce, “Ka faɗi daidai, malam!”
- Luka 20:40kusan 33 M.
Kuma ba wanda ya sami ƙarfin halin yin masa waɗansu tambayoyi.