Tsallake zuwa abun ciki

Ayoyin Littafi Mai Tsarki game da Psalms

896 ayoyi · 16 fannoni

Mahimman ayoyin Littafi Mai Tsarki

Tace bisa littafi
  1. Ya Ubangiji Maɗaukaki, mai albarka ne mutumin da ya dogara gare ka.

  2. Na ’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Waƙa ce. Ya kafa harsashinsa a kan dutse mai tsarki.

  3. Ubangiji yana ƙaunar ƙofofin Sihiyona fiye da dukan wuraren zaman Yaƙub.

  4. Ana faɗin abubuwa masu ɗaukaka game da ke Ya birnin Allah, Sela

  5. “Zan lissafta Rahab a cikin waɗanda suka san ni, Filistiya ita ma, da Taya, tare da Kush, zan kuma ce, ‘An haifi wannan a Sihiyona.’ ”

  6. Tabbatacce, game da Sihiyona za a ce, “Wannan da wancan an haifa a cikinta, Mafi Ɗaukaka kansa zai kafa ta.”

  7. Ubangiji zai rubuta a littafin sunayen mutanensa, “An haifi wannan a Sihiyona.” Sela

  8. Yayinda suke kaɗe-kaɗe za su rera, “Dukan maɓulɓulaina suna cikinki.”

  9. Zabura ce. Waƙa ce. Domin ranar Asabbaci. Yana da kyau a yabi Ubangiji a kuma yi kiɗi ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka,

  10. don a yi shelar ƙaunarka da safe amincinka kuma da dare,

  11. da kiɗin molo mai tsirkiya goma da kuma ƙarar garaya.

  12. Gama ka sa na yi murna ta wurin ayyukanka, ya Ubangiji; na rera don farin ciki saboda ayyukan hannuwanka.

  13. Ina misalin ayyukanka, ya Ubangiji, tunaninka da zurfi suke ƙwarai!

  14. Mutum marar azanci ba zai sani ba, wawa ba zai gane ba,

  15. cewa ko da yake mugaye suna girma kamar ciyawa kuma dukan masu aikata mugunta suna haɓaka, za a hallaka su har abada.

  16. Amma kai, ya Ubangiji, za a ɗaukaka har abada.

  17. Gama tabbatacce abokan gābanka, ya Ubangiji, tabbatacce abokan gābanka za su hallaka; za a watsar da dukan masu aikata mugunta.

  18. Ka ɗaukaka ƙahona kamar na ɓauna; an zubo mai masu kyau a kaina.

  19. Idanuna sun ga fāɗuwar maƙiyana; kunnuwana sun ji kukan mugayen maƙiyana.

  20. Adalai za su haɓaka kamar itacen dabino, za su yi girma kama al’ul na Lebanon;

  21. da aka daddasa a gidan Ubangiji, za su haɓaka a filayen gidan Allahnmu.

  22. Za su ci gaba da ba da ’ya’ya a tsufansu, za su kasance ɗanye kuma kore shar,

  23. suna shela cewa, “Ubangiji adali ne; shi ne Dutsena, kuma babu mugunta a cikinsa.”

  24. Ubangiji yana mulki, yana sanye da ɗaukaka; Ubangiji yana sanye da ɗaukaka yana kuma sanye da ƙarfi. An kafa duniya daram; ba za a iya matsar da ita ba.

  25. An kafa kursiyin tun da daɗewa; kana nan tun fil azal.