Skip to content

Ayoyin Littafi Mai Tsarki game da Miracles

338 ayoyi · 37 fannoni

Mahimman ayoyin Littafi Mai Tsarki

Tace bisa littafi
  1. Da gangan suka gwada Allah ta wurin neman abincin da suke kwaɗayi.

  2. Suka yi magana a kan Allah, suna cewa, “Allah zai iya shimfiɗa tebur a cikin hamada?

  3. Sa’ad da ya bugi dutse, ruwa ya ɓulɓulo, rafuffuka suka yi gudu a yalwace. Amma zai iya ba mu abinci? Zai iya tanada wa mutanensa nama?”

  4. Sa’ad da Ubangiji ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; wutarsa ta ɓarke a kan Yaƙub, hasalarsa kuwa ta tashi a kan Isra’ila,

  5. gama ba su gaskata ga Allah ba ko su dogara ga cetonsa.

  6. Duk da haka ya ba da umarni ga sarari a bisa ya kuma buɗe ƙofofin sammai;

  7. ya sauko da Manna wa mutanensa don su ci, ya ba su hatsin sama.

  8. Mutane suka ci burodin mala’iku; ya aika musu dukan abincin da za su iya ci.

  9. Ya saki iskar gabas daga sammai ya kuma saki iskar yamma ta wurin ikonsa.

  10. Ya sauko da nama a kansu kamar ƙura, tsuntsaye masu firiya kamar yashi a bakin teku.

  11. Ya sa suka sauka a cikin sansaninsu, ko’ina kewaye da tentunansu.

  12. Suka ci har suka sami fiye da abin da ya ishe su, gama ya ba su abin da suka yi kwaɗayi.

  13. Amma kafin su juyo daga abincin da suka yi kwaɗayi, kai tun ma yana a bakunansu,

  14. fushin Allah ya ƙuna a kansu; ya karkashe waɗanda suka fi ƙiba a cikinsu, yana yankan matasan Isra’ila.

  15. Duk da haka, suka ci gaba da yin zunubi; duk da abubuwan banmamakinsa, ba su gaskata ba.

  16. Ku tuna da abubuwan mamakin da ya yi, mu’ujizansa, da kuma hukunce-hukuncen da ya zartar,

  17. Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.

  18. Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.

  19. Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.

  20. Ruwaye suka rufe abokan gābansu; babu ko ɗaya da ya tsira.

  21. Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.

  22. Saboda haka zan firgita waɗannan mutane sau ɗaya da abubuwan banmamaki a kan abubuwan banmamaki; hikimar masu hikima za tă lalace, azancin masu azanci zai ɓace.”

  23. Ka aikata ayyukan banmamaki da kuma al’ajabai a Masar ka kuma ci gaba da su har yă zuwa yau, a Isra’ila da kuma a cikin dukan ’yan adam, ka kuma sami sunan da har yanzu yake naka.

  24. Ka fitar da mutanenka Isra’ila daga Masar da alamu da abubuwa banmamaki, ta wurin hannu mai iko da kuma hannu mai ƙarfi tare da banrazana mai girma.

  25. Sarki ya kuma ce wa Daniyel, “Tabbatacce Allahnka shi ne Allahn alloli da kuma Sarkin sarakuna da mai bayyana asirai, gama ka iya bayyana wannan asiri.”