Tsallake zuwa abun ciki

circa 6 BC – AD 30

The Life of Jesus

The eternal Son of God enters history: born in Bethlehem, baptized in the Jordan, crucified at Golgotha, raised on the third day.

3,779 ayoyi · 4 littattafai da aka rufe

Ayoyi daga wannan lokacin

Tace bisa littafi
  1. Yohanna 12:15kusan 33 M.

    “Kada ki ji tsoro, ya Diyar Sihiyona; duba, ga sarkinki yana zuwa, zaune a kan aholaki jaki.”

  2. Yohanna 12:16kusan 33 M.

    Da fari almajiransa ba su gane dukan wannan ba. Sai bayan da aka ɗaukaka Yesu, sa’an nan suka gane cewa an rubuta waɗannan abubuwa game da shi ne, har ma suka yi masa waɗannan abubuwa.

  3. Yohanna 12:17kusan 33 M.

    Taron da suke tare da shi a sa’ad da ya kira Lazarus daga kabari ya kuma tā da shi daga matattu suka yi ta baza labarin.

  4. Yohanna 12:18kusan 33 M.

    Mutane da yawa kuwa suka fita taryensa, saboda sun ji labarin abin banmamakin da ya yi.

  5. Yohanna 12:19kusan 33 M.

    Saboda haka Farisiyawa suka ce wa juna, “Duba, wannan ba ya kai mu ko’ina. Ga shi, duk duniya tana bin sa!”

  6. Yohanna 12:20kusan 33 M.

    To, akwai waɗansu Hellenawa a cikin waɗanda suka haura don su yi sujada a Bikin.

  7. Yohanna 12:21kusan 33 M.

    Suka zo wurin Filibus, wanda yake daga Betsaida ta Galili, da roƙo. Suka ce, “Ranka yă daɗe, muna so mu ga Yesu.”

  8. Yohanna 12:22kusan 33 M.

    Sai Filibus ya je ya gaya wa Andarawus, Andarawus da kuma Filibus suka gaya wa Yesu.

  9. Yohanna 12:23kusan 33 M.

    Yesu ya amsa ya ce, “Lokaci ya yi da za a ɗaukaka Ɗan Mutum.

  10. Yohanna 12:24kusan 33 M.

    Gaskiya nake gaya muku, sai ƙwayar alkama ta fāɗi ƙasa ta mutu, in ba haka ba za tă kasance ƙwaya ɗaya tak. Amma in ta mutu, za tă ba da ’ya’ya da yawa.

  11. Yohanna 12:25kusan 33 M.

    Duk mai ƙaunar ransa, zai rasa shi, duk mai ƙin ransa a wannan duniya, zai kiyaye shi har yă zuwa rai madawwami.

  12. Yohanna 12:26kusan 33 M.

    Duk wanda zai bauta mini dole yă bi ni, inda kuma nake, a can bawana zai kasance. Ubana zai girmama wanda yake bauta mini.

  13. Yohanna 12:27kusan 33 M.

    “Yanzu kuwa na damu, amma me zan ce? ‘Uba, ka cece ni daga wannan sa’a’? A’a, ai, saboda wannan dalili ne musamman na zo.

  14. Yohanna 12:28kusan 33 M.

    Uba, ka ɗaukaka sunanka!” Sai wata murya ta fito daga sama ta ce, “Na riga na ɗaukaka shi, zan kuma ƙara ɗaukaka shi.”

  15. Yohanna 12:29kusan 33 M.

    Taron da suke a wurin suka ji, suka ce an yi tsawa; waɗansu kuwa suka ce mala’ika ne ya yi masa magana.

  16. Yohanna 12:30kusan 33 M.

    Yesu ya ce, “An yi wannan muryar saboda amfaninku ne, ba don nawa ba.

  17. Yohanna 12:31kusan 33 M.

    Yanzu ne za a yi wa duniyan nan shari’a, yanzu ne za a tumɓuke mai mulkin duniyan nan.

  18. Yohanna 12:32kusan 33 M.

    Amma ni, sa’ad da aka ɗaga ni daga ƙasa, zan ja dukan mutane gare ni.”

  19. Yohanna 12:33kusan 33 M.

    Ya faɗa haka ne don yă nuna irin mutuwar da zai yi.

  20. Yohanna 12:34kusan 33 M.

    Sai taron suka ce, “Ahab, Dokarmu ta gaya mana cewa, Kiristi zai kasance har abada, to, yaya za ka ce, ‘Dole ne a ɗaga Ɗan Mutum?’ Wane ne wannan ‘Ɗan Mutum’?”

  21. Yohanna 12:35kusan 33 M.

    Sai Yesu ya ce musu, “Haske zai kasance da ku na ɗan lokaci. Ku yi tafiya yayinda hasken yana nan tare da ku, kada duhu yă cim muku. Mai tafiya a cikin duhu bai san inda za shi ba.

  22. Yohanna 12:36kusan 33 M.

    Ku dogara ga hasken yayinda kuke da shi, don ku zama ’ya’yan haske.” Da Yesu ya gama magana, sai ya tafi ya ɓuya daga gare su.

  23. Yohanna 12:37kusan 33 M.

    Ko bayan Yesu ya yi dukan waɗannan abubuwan banmamaki a gabansu, duk da haka ba su gaskata da shi ba.

  24. Yohanna 12:38kusan 33 M.

    Wannan ya faru ne, don a cika maganar annabi Ishaya cewa, “Ubangiji, wa ya gaskata saƙonmu, ga wa kuma aka bayyana hannun ikon Ubangiji?”

  25. Yohanna 12:39kusan 33 M.

    Saboda haka ba su iya gaskatawa ba, domin, kamar yadda Ishaya ya faɗa a wani wuri cewa,