circa 6 BC – AD 30
The Life of Jesus
The eternal Son of God enters history: born in Bethlehem, baptized in the Jordan, crucified at Golgotha, raised on the third day.
Ayoyi daga wannan lokacin
- Yohanna 11:22kusan 33 M.
Amma na san cewa ko yanzu ma Allah zai ba ka duk abin da ka roƙa.”
- Yohanna 11:23kusan 33 M.
Yesu ya ce mata, “Ɗan’uwanki zai sāke tashi.”
- Yohanna 11:24kusan 33 M.
Marta ta amsa ta ce, “Na sani zai sāke tashi a tashin matattu a rana ta ƙarshe.”
- Yohanna 11:25kusan 33 M.
Yesu ya ce mata, “Ni ne tashin matattu da kuma rai. Duk wanda ya gaskata da ni zai rayu, ko ya mutu;
- Yohanna 11:26kusan 33 M.
kuma duk wanda yake raye ya kuma gaskata da ni ba zai taɓa mutuwa ba. Kin gaskata wannan?”
- Yohanna 11:27kusan 33 M.
Sai ta ce masa, “I, Ubangiji, na gaskata kai ne Kiristi, Ɗan Allah, mai zuwa cikin duniya.”
- Yohanna 11:28kusan 33 M.
Bayan ta faɗa haka kuwa, sai ta koma ta je ta kira ’yar’uwarta Maryamu a gefe. Ta ce, “Ga Malam ya zo, kuma yana kiranki.”
- Yohanna 11:29kusan 33 M.
Sa’ad da Maryamu ta ji haka sai ta yi wuf ta tafi wurinsa.
- Yohanna 11:30kusan 33 M.
Yesu dai bai riga ya shiga ƙauyen ba tukuna, har yanzu yana inda Marta ta tarye shi.
- Yohanna 11:31kusan 33 M.
Da Yahudawan da suke tare da Maryamu a cikin gida, suke mata ta’aziyya, suka ga ta yi wuf ta fita, sai suka bi ta, suna tsammani za tă kabarin ne tă yi kuka a can.
- Yohanna 11:32kusan 33 M.
Sa’ad da Maryamu ta kai inda Yesu yake, ta kuma gan shi, sai ta fāɗi a gabansa ta ce, “Ubangiji, da kana nan, da ɗan’uwana bai mutu ba.”
- Yohanna 11:33kusan 33 M.
Da Yesu ya ga tana kuka, Yahudawan da suka zo tare da ita ma suna kuka, sai ya yi juyayi ƙwarai a ruhu ya kuma damu.
- Yohanna 11:34kusan 33 M.
Sai ya yi tambaya ya ce, “Ina kuka sa shi?” Suka amsa suka ce, “Ubangiji zo ka gani.”
- Yohanna 11:35kusan 33 M.
Yesu ya yi kuka.
- Yohanna 11:36kusan 33 M.
Sai Yahudawa suka ce, “Dubi yadda yake ƙaunarsa!”
- Yohanna 11:37kusan 33 M.
Amma waɗansunsu suka ce, “Anya, wanda ya buɗe wa makahon nan idanu, ba zai iya yin wani abu yă hana wannan mutum mutuwa ba?”
- Yohanna 11:38kusan 33 M.
Yesu, har yanzu cike da juyayi, ya zo kabarin. Kogo ne da aka rufe bakin da dutse.
- Yohanna 11:39kusan 33 M.
Sai Yesu ya ce, “Ku kawar da dutsen.” Marta, ’yar’uwan mamacin ta ce, “Ubangiji, yanzu, ai, zai yi wari, don yau kwanansa huɗu ke nan a can.”
- Yohanna 11:40kusan 33 M.
Sai Yesu ya ce, “Ban gaya miki cewa in kin gaskata za ki ga ɗaukakar Allah ba?”
- Yohanna 11:41kusan 33 M.
Saboda haka suka kawar da dutsen. Sa’an nan Yesu ya dubi sama ya ce, “Uba, na gode maka da ka saurare ni.
- Yohanna 11:42kusan 33 M.
Na san kullum kakan saurare ni, na dai faɗa haka ne saboda amfanin mutanen nan da suke tsaitsaye, don su gaskata cewa kai ka aiko ni.”
- Yohanna 11:43kusan 33 M.
Sa’ad da ya faɗa haka, sai Yesu ya yi kira da babbar murya ya ce, “Lazarus, ka fito!”
- Yohanna 11:44kusan 33 M.
Sai mamacin ya fito, hannuwansa da ƙafafunsa a daure da ƙyallayen lilin, fuskarsa kuwa an naɗe da mayafi. Yesu ya ce musu, “Ku tuɓe kayan bizo, ku bar shi yă tafi.”
- Yohanna 11:45kusan 33 M.
Saboda haka Yahudawa da yawa da suka zo don su ziyarci Maryamu, suka kuma ga abin da Yesu ya yi, suka ba da gaskiya gare shi.
- Yohanna 11:46kusan 33 M.
Amma waɗansunsu suka je wurin Farisiyawa suka gaya musu abin da Yesu ya yi.