Tsallake zuwa abun ciki

circa 605–538 BC

The Babylonian Exile

Jerusalem falls and the temple burns; Ezekiel and Daniel minister among the exiles as Lamentations mourns the city's ruin.

1,784 ayoyi · 3 littattafai da aka rufe

Ayoyi daga wannan lokacin

Tace bisa littafi
  1. Ezekiyel 47:7kusan 574 K.H.

    Sa’ad da na iso can, sai na ga itatuwa masu yawa a kowane gefen kogin.

  2. Ezekiyel 47:8kusan 574 K.H.

    Sai ya ce mini, “Wannan ruwa yana malalowa zuwa yankin gabas ya kuma gangaro zuwa cikin Araba, inda zai shiga Teku. Sa’ad da ya shiga cikin Tekun sai ruwan a can ya zama mai daɗi.

  3. Ezekiyel 47:9kusan 574 K.H.

    Tarin halittu masu rai za su rayu a duk inda ruwan ya malalo. Za a kasance da kifi masu yawa, domin wannan ruwa yana malalowa a can yana kuma mai da ruwan gishiri yă zama ruwa mai daɗi; saboda haka duk inda ruwan ya malalo, kome zai rayu.

  4. Ezekiyel 47:10kusan 574 K.H.

    Masunta za su tsaya a gaɓar; daga En Gedi zuwa En Eglayim, za a kasance da wuraren jefa abin kamun kifi. Za a sami kifayen iri-iri, kamar kifaye Bahar Rum.

  5. Ezekiyel 47:11kusan 574 K.H.

    Amma fadamun da tafkunan ba za su zama masu daɗi ba; za a bar su a gishirinsu.

  6. Ezekiyel 47:12kusan 574 K.H.

    ’Ya’yan itatuwa na kowane iri za su yi girma a kowane gefen kogin. Ganyayensu ba su bushe ba, ba kuwa za su fasa yin ’ya’ya ba. Kowane wata za su ba da ’ya’ya domin ruwa daga wuri mai tsarki yana malalo musu. ’Ya’yansu za su zama abinci, ganyayensu kuma za su zama magani.”

  7. Ezekiyel 47:13kusan 574 K.H.

    Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Waɗannan su ne iyakokin da za ku raba ƙasar gādo cikin kabilan Isra’ila goma sha biyu, da rabo biyu don Yusuf.

  8. Ezekiyel 47:14kusan 574 K.H.

    Za ku raba ta daidai a cikinsu. Gama na ɗaga hannu na rantse zan ba da ita ga kakanninku, wannan ƙasa za tă zama gādonku.

  9. Ezekiyel 47:15kusan 574 K.H.

    “Wannan ce za tă zama iyakar ƙasa. “A wajen arewa za tă fara daga Bahar Rum ta hanyar Hetlon ta wuce Lebo Hamat zuwa Zedad,

  10. Ezekiyel 47:16kusan 574 K.H.

    Berota da Sibrayim (wadda take a iyaka tsakanin Damaskus da Hamat), har zuwa Hazer-Hattikon, wadda take a iyakar Hauran.

  11. Ezekiyel 47:17kusan 574 K.H.

    Iyakar za tă miƙe daga teku zuwa Hazar-Enon, ta iyakar Damaskus, da iyakar Hamat a arewa. Wannan ita ce iyakar a wajen arewa.

  12. Ezekiyel 47:18kusan 574 K.H.

    A wajen gabas iyakar za tă kama tsakanin Hauran da Damaskus, ta bi ta Urdun tsakanin Gileyad da ƙasar Isra’ila, zuwa tekun gabas har zuwa Tamar. Wannan ita ce iyakar a wajen gabas.

  13. Ezekiyel 47:19kusan 574 K.H.

    A wajen kudu za tă fara daga Tamar har zuwa ruwan Meriba Kadesh, sa’an nan ta bi Rafin Masar zuwa Bahar Rum. Wannan ita ce iyakar a wajen kudu.

  14. Ezekiyel 47:20kusan 574 K.H.

    A wajen yamma, Bahar Rum ne zai zama iyakar zuwa wani wuri ɗaura da Lebo Hamat. Wannan ita ce iyakar a wajen yamma.

  15. Ezekiyel 47:21kusan 574 K.H.

    “Za ku rarraba wannan ƙasa a tsakaninku bisa ga kabilan Isra’ila.

  16. Ezekiyel 47:22kusan 574 K.H.

    Za ku raba ta kamar gādo wa kanku da kuma wa baƙin da suka zauna a cikinku waɗanda suke da ’ya’ya. Za ku ɗauka su kamar ’yan ƙasa haifaffun Isra’ilawa; za su yi gādo tare da ku a cikin kabilan Isra’ila.

  17. Ezekiyel 47:23kusan 574 K.H.

    A duk kabilar da baƙon yake zama, a can za ku ba shi gādonsa,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.

  18. Ezekiyel 48:1kusan 574 K.H.

    “Ga kabilan, a jere bisa ga sunayensu. “A iyaka ta arewa, Dan zai sami rabo; zai bi hanyar Hetlon zuwa Lebo Hamat. Hazar-Enan da iyakar arewancin Damaskus kusa da Hamat za tă zama sashen iyakarsa a wajen gabas zuwa wajen yamma.

  19. Ezekiyel 48:2kusan 574 K.H.

    Asher zai sami rabo; zai yi iyaka da yankin Dan daga gabas zuwa yamma.

  20. Ezekiyel 48:3kusan 574 K.H.

    Naftali zai sami rabo; zai yi iyaka da yankin Asher daga gabas zuwa yamma.

  21. Ezekiyel 48:4kusan 574 K.H.

    Manasse zai sami rabo; zai yi iyaka da yankin Naftali daga gabas zuwa yamma.

  22. Ezekiyel 48:5kusan 574 K.H.

    Efraim zai sami rabo; zai yi iyaka da yankin Manasse daga gabas zuwa yamma.

  23. Ezekiyel 48:6kusan 574 K.H.

    Ruben zai sami rabo; zai yi iyaka da Efraim daga gabas zuwa yamma.

  24. Ezekiyel 48:7kusan 574 K.H.

    Yahuda zai sami rabo; zai yi iyaka da yankin Ruben daga gabas zuwa yamma.

  25. Ezekiyel 48:8kusan 574 K.H.

    “Kusa da yankin Yahuda daga gabas zuwa yamma zai zama rabon da za ku bayar a matsayin kyauta ta musamman. Faɗinsa zai zama kamu 25,000, tsawonsa kuma zai zama daidai da tsawon yankunan kabilu daga gabas zuwa yamma; wuri mai tsarki zai kasance a tsakiyar wannan yanki.