Tsallake zuwa abun ciki

Ayoyin Littafi Mai Tsarki game da The Punishment of the Wicked

157 ayoyi · 57 fannoni

Mahimman ayoyin Littafi Mai Tsarki

Tace bisa littafi
  1. Amma Allah zai harbe su da kibiyoyi; nan da nan za a buge su su fāɗi.

  2. Gama na yi kishin masu girman kai sa’ad da na ga cin gaban da masu mugunta suke yi.

  3. Ba sa yin wata fama; jikunansu lafiya suke da kuma ƙarfi.

  4. Ba sa shan wata wahalar da sauran mutane ke sha; ba su da damuwa irin na ’yan adam.

  5. Saboda girman kai ya zama musu abin wuya; tā da hankali ya zama musu riga.

  6. Daga mugayen zukatansu laifi kan fito mugaye ƙulle-ƙullen da suke cikin zukatansu ba su da iyaka.

  7. Suna ba’a, suna faɗin mugayen abubuwa; cikin girman kan suna barazana yin danniya.

  8. Bakunansu na cewa sama na su ne, kuma harsunansu sun mallaki duniya.

  9. Saboda haka mutanensu sun juya gare su suna kuma shan ruwa a yalwace.

  10. Suna cewa, “Yaya Allah zai sani? Mafi Ɗaukaka yana da sani ne?”

  11. Ga yadda mugaye suke, kullum ba su da damuwa, arzikinsu yana ta ƙaruwa.

  12. Tabbatacce a banza na bar zuciyata da tsabta; a banza na wanke hannuwa don nuna rashin laifi.

  13. Dukan yini na sha annoba; an hukunta ni kowace safiya.

  14. Da na ce, “Zan faɗa haka,” da na bashe ’ya’yanka.

  15. Sa’ad da na yi ƙoƙari in gane wannan, sai ya zama danniya a gare ni

  16. sai da na shiga wuri mai tsarki na Allah; sa’an nan na gane abin da ƙarshensu zai zama.

  17. Tabbatacce ka sa su a ƙasa mai santsi; ka jefar da su ga hallaka.

  18. Duba yadda suka hallaka farat ɗaya, razana ta share su gaba ɗaya!

  19. Ya shirya hanya wa fushinsa; bai tsare ransu daga mutuwa ba amma ya miƙa su ga annoba.

  20. Za ka dai gan da idanunka yadda ake hukunta mugaye.

  21. cewa ko da yake mugaye suna girma kamar ciyawa kuma dukan masu aikata mugunta suna haɓaka, za a hallaka su har abada.

  22. Zai sāka musu saboda zunubansu yă kuma hallaka su saboda muguntarsu; Ubangiji Allahnmu zai hallaka su.

  23. ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani, saboda muguntar waɗanda suka zauna a can.

  24. Ka tabbata da wannan. Mugaye ba za su tafi babu hukunci ba, amma waɗanda suke masu adalci za su tafi babu hukunci.

  25. In masu adalci sun sami abin da ya dace da su a duniya, yaya zai zama ga marasa sanin Allah da kuma masu zunubi!