Tsallake zuwa abun ciki

circa 1010–970 BC

The Reign of David

David unites the tribes, conquers Jerusalem, and establishes Israel's golden age—even through deep personal failure.

1,230 ayoyi · 2 littattafai da aka rufe

Ayoyi daga wannan lokacin

Tace bisa littafi
  1. 2 Sama’ila 21:18kusan 1018 K.H.

    Ana nan, sai aka sāke yin wani yaƙin da Filistiyawa, a Gob. A lokacin Sibbekai mutumin Husha ya kashe Saf, wani daga zuriyar Rafa.

  2. 2 Sama’ila 21:19kusan 1018 K.H.

    Sai aka sāke yin wani yaƙin da Filistiyawa a Gob, Elhanan ɗan Ya’are-Oregim mutumin Betlehem ya kashe Goliyat mutumin Gat, wanda girmar sandan māshinsa ta yi kama da taɓarya.

  3. 2 Sama’ila 21:20kusan 1018 K.H.

    Har wa yau a wani yaƙin da aka yi a Gat, akwai wani ƙaton mutum mai yatsotsi shida a kowane hannu, da kuma yatsotsi shida a kowane ƙafa, yatsotsi ashirin da huɗu ke nan. Shi ma daga zuriya Rafa ne.

  4. 2 Sama’ila 21:21kusan 1018 K.H.

    Da ya yi wa Isra’ila reni, sai Yonatan ɗan Shimeya, ɗan’uwa Dawuda, ya kashe shi.

  5. 2 Sama’ila 21:22kusan 1018 K.H.

    Waɗannan huɗu zuriyar Rafa ne a Gat, suka kuwa mutu ta hannu Dawuda da mutanensa.

  6. 2 Sama’ila 22:1kusan 1018 K.H.

    Dawuda ya rera wannan waƙa ga Ubangiji, sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa, da kuma daga hannun Shawulu.

  7. 2 Sama’ila 22:2kusan 1018 K.H.

    Ya ce, “Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona;

  8. 2 Sama’ila 22:3kusan 1018 K.H.

    Allahna shi ne dutsena. A gare shi nake samun kāriya shi ne garkuwata da kuma ƙahon cetona. Shi ne mafakata, maɓuyata, da mai cetona. Daga mutane masu fitina, ka cece ni.

  9. 2 Sama’ila 22:4kusan 1018 K.H.

    “Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa tsira daga abokan gābana.

  10. 2 Sama’ila 22:5kusan 1018 K.H.

    Raƙumar ruwan mutuwa sun kewaye ni; raƙumar ruwan hallaka suna cin ƙarfina.

  11. 2 Sama’ila 22:6kusan 1018 K.H.

    Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe ni; tarkuna kuma suka auka mini.

  12. 2 Sama’ila 22:7kusan 1018 K.H.

    “A cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; na yi kira ga Allahna. Daga cikin haikalinsa ya saurare muryata; kukata ta zo kunnensa.

  13. 2 Sama’ila 22:8kusan 1018 K.H.

    Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, harsashan sararin sama sun jijjigu; suka yi makyarkyata saboda yana fushi.

  14. 2 Sama’ila 22:9kusan 1018 K.H.

    Hayaƙi ya taso daga kafaffen hancinsa; harshen wuta mai cinyewa daga bakinsa, garwashi mai ƙuna daga bakinsa.

  15. 2 Sama’ila 22:10kusan 1018 K.H.

    Ya buɗe sararin sama, ya sauko ƙasa, girgije mai duhu suna ƙarƙashin ƙafafunsa.

  16. 2 Sama’ila 22:11kusan 1018 K.H.

    Ya hau kerubobi, ya tashi sama; ya yi firiya a fikafikan iska.

  17. 2 Sama’ila 22:12kusan 1018 K.H.

    Ya mai da duhu abin rufuwarsa gizagizai masu kauri cike da ruwa suka kewaye shi.

  18. 2 Sama’ila 22:13kusan 1018 K.H.

    Daga cikin hasken gabansa garwashi wuta mai ci ya yi walƙiya.

  19. 2 Sama’ila 22:14kusan 1018 K.H.

    Ubangiji ya yi tsawa daga sararin sama; aka ji muryar Mafi Ɗaukaka.

  20. 2 Sama’ila 22:15kusan 1018 K.H.

    Ya harbe kibiyoyi, ya wartsar da abokan gāba, da walƙiya kuma ya sa suka gudu.

  21. 2 Sama’ila 22:16kusan 1018 K.H.

    Aka bayyana kwarin teku, tushen duniya suka tonu. A tsawatawar Ubangiji, da numfashinsa mai ƙarfi daga hancinsa.

  22. 2 Sama’ila 22:17kusan 1018 K.H.

    “Daga sama ya miƙo hannu ya ɗauke ni, ya tsamo ni daga zurfafa ruwaye.

  23. 2 Sama’ila 22:18kusan 1018 K.H.

    Ya kuɓutar da ni daga hannun abokin gāba mai iko, daga maƙiyina da suka fi ƙarfina.

  24. 2 Sama’ila 22:19kusan 1018 K.H.

    Suka auka mini cikin ranar masifata, amma Ubangiji ya kiyaye ni.

  25. 2 Sama’ila 22:20kusan 1018 K.H.

    Ya fito da ni, ya kai ni wuri mafi fāɗi; ya kuɓutar da ni gama yana jin daɗina.