Tsallake zuwa abun ciki

circa 6 BC – AD 30

The Life of Jesus

The eternal Son of God enters history: born in Bethlehem, baptized in the Jordan, crucified at Golgotha, raised on the third day.

3,779 ayoyi · 4 littattafai da aka rufe

Ayoyi daga wannan lokacin

Tace bisa littafi
  1. Markus 15:19kusan 33 M.

    Suka dinga bugunsa a kā da sanda, suka tattofa masa miyau. Suka durƙusa suka yi masa bangirma na ba’a.

  2. Markus 15:20kusan 33 M.

    Bayan da suka gama yin masa ba’a, suka tuɓe rigar mai ruwan shunayyar, suka sa masa nasa tufafi. Sai suka tafi da shi don a gicciye shi.

  3. Markus 15:21kusan 33 M.

    Sai ga wani mutum daga Sairin da ake kira Siman, mahaifin Alekzanda da Rufus, yana wucewa kan hanyarsa daga ƙauye. Sai suka tilasta shi yă ɗauki gicciyen.

  4. Markus 15:22kusan 33 M.

    Suka kawo Yesu a wurin da ake kira Golgota (wanda yake nufin Wurin Ƙoƙon Kai).

  5. Markus 15:23kusan 33 M.

    Sai suka miƙa masa ruwan inabi gauraye da mur, don yă rage zafi, amma bai sha ba.

  6. Markus 15:24kusan 33 M.

    Sai suka gicciye shi. Suka rarraba tufafinsa, suka jefa ƙuri’a a kansu don su ga abin da kowa zai samu.

  7. Markus 15:25kusan 33 M.

    Sa’a ta uku na safe ce kuwa aka gicciye shi.

  8. Markus 15:26kusan 33 M.

    Akwai rubutu na zarginsa, da ya ce, Sarkin Yahudawa.

  9. Markus 15:27kusan 33 M.

    Suka gicciye ’yan fashi biyu tare da shi, ɗaya a damansa, ɗayan kuma a hagunsa.

  10. Markus 15:28kusan 33 M.

    And the scripture was fulfilled, which saith, And he was numbered with the transgressors.

  11. Markus 15:29kusan 33 M.

    Masu wucewa suka zazzage shi. Suka kaɗa kai suna cewa, “To, kai da za ka rushe haikali ka kuma gina shi a kwana uku,

  12. Markus 15:30kusan 33 M.

    sai ka sauko daga gicciyen, ka ceci kanka!”

  13. Markus 15:31kusan 33 M.

    Haka kuma, manyan firistoci da malaman dokoki suka yi masa ba’a a junansu, suna cewa, “Ya ceci waɗansu, amma ya kāsa ceton kansa!

  14. Markus 15:32kusan 33 M.

    Bari wannan Kiristi, wannan Sarkin Isra’ila, yă sauko yanzu daga gicciye, don mu ga mu kuma gaskata.” Waɗanda aka gicciye tare da shi ma suka zazzage shi.

  15. Markus 15:33kusan 33 M.

    Daga sa’a ta shida har zuwa sa’a ta tara na rana, duhu ya rufe dukan ƙasar.

  16. Markus 15:34kusan 33 M.

    A daidai sa’a ta tara na rana, sai Yesu ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce, “Eloi, Eloi, lama sabaktani?” (Wato, “Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni?”).

  17. Markus 15:35kusan 33 M.

    Da waɗansu cikin waɗanda suke tsattsaye kusa da wurin suka ji haka, suka ce, “Ku saurara, yana kiran Iliya.”

  18. Markus 15:36kusan 33 M.

    Wani mutum ya ruga ya je ya jiƙo soso da ruwan tsami, ya soka a sanda ya miƙa wa Yesu yă sha. Ya ce, “Ku ƙyale shi. Bari mu ga ko Iliya zai zo yă saukar da shi.”

  19. Markus 15:37kusan 33 M.

    Da murya mai ƙarfi, Yesu ya ja numfashinsa na ƙarshe.

  20. Markus 15:38kusan 33 M.

    Labulen haikali kuwa ya yage kashi biyu, daga sama har ƙasa.

  21. Markus 15:39kusan 33 M.

    Da jarumin da yake tsaye a gaban Yesu ya ji muryarsa, ya kuma ga yadda ya mutu, sai ya ce, “Gaskiya, wannan mutum Ɗan Allah ne!”

  22. Markus 15:40kusan 33 M.

    Waɗansu mata suna kallo daga nesa. A cikinsu kuwa akwai Maryamu Magdalin, Maryamu mahaifiyar Yaƙub ƙarami da Yusuf, da kuma Salome.

  23. Markus 15:41kusan 33 M.

    A Galili waɗannan mata ne suka riƙa bin sa suna yin masa hidima. Waɗansu mata da yawa da suka zo tare da shi daga Urushalima, su ma suna nan a can.

  24. Markus 15:42kusan 33 M.

    Ranar kuwa ita ce ranar Shirye-shirye (wato, ana kashegari Asabbaci). Saboda haka, da yamma ta yi, sai

  25. Markus 15:43kusan 33 M.

    Yusuf daga Arimateya, wani sanannen ɗan Majalisa, wanda dā ma yake jiran zuwan mulkin Allah, ya je wajen Bilatus ba tsoro, ya roƙa a ba shi jikin Yesu.