Tsallake zuwa abun ciki

circa 6 BC – AD 30

The Life of Jesus

The eternal Son of God enters history: born in Bethlehem, baptized in the Jordan, crucified at Golgotha, raised on the third day.

3,779 ayoyi · 4 littattafai da aka rufe

Ayoyi daga wannan lokacin

Tace bisa littafi
  1. Markus 14:41kusan 33 M.

    Da ya koma sau na uku, sai ya ce musu, “Har yanzu kuna barci, kuna hutawa ba? Ya isa! Lokaci ya yi. Duba an ba da Ɗan Mutum a hannun masu zunubi.

  2. Markus 14:42kusan 33 M.

    Ku tashi! Mu tafi! Ga mai bashe ni ɗin yana zuwa!”

  3. Markus 14:43kusan 33 M.

    Yana cikin magana ke nan, sai Yahuda, ɗaya daga cikin Sha Biyun ya bayyana. Ya zo tare da taro da suke riƙe da takuba da sanduna. Manyan firistoci da malaman dokoki, da kuma dattawa ne suka turo taron.

  4. Markus 14:44kusan 33 M.

    Mai bashe shi ɗin ya riga ya shirya alama da su cewa, “Wanda na yi wa sumba, shi ne mutumin, ku kama shi, ku riƙe sosai.”

  5. Markus 14:45kusan 33 M.

    Nan da nan Yahuda ya je wurin Yesu ya ce, “Rabbi!” Ya kuma yi masa sumba.

  6. Markus 14:46kusan 33 M.

    Mutanen kuwa suka kama Yesu, suka riƙe shi.

  7. Markus 14:47kusan 33 M.

    Sai wani cikin waɗanda suke tsattsaye kusa ya zāre takobinsa, ya sare kunnen bawan babban firist.

  8. Markus 14:48kusan 33 M.

    Yesu ya ce, “Ina jagoran wani tawaye ne da kuka fito da takuba da kuma sanduna domin ku kama ni?

  9. Markus 14:49kusan 33 M.

    Kowace rana ina tare da ku, ina koyarwa a filin haikali, ba ku kama ni ba. Amma dole a cika Nassi.”

  10. Markus 14:50kusan 33 M.

    Sai kowa ya yashe shi ya gudu.

  11. Markus 14:51kusan 33 M.

    Wani saurayin da ba ya sanye da kome sai rigar lilin, yana bin Yesu. Da suka yi ƙoƙarin kama shi,

  12. Markus 14:52kusan 33 M.

    sai ya gudu ya bar rigarsa, ya gudu tsirara.

  13. Markus 14:53kusan 33 M.

    Suka kai Yesu wajen babban firist, sai dukan manyan firistoci, dattawa da kuma malaman dokoki suka taru.

  14. Markus 14:54kusan 33 M.

    Bitrus ya bi shi daga nesa, har cikin filin gidan babban firist. A can, ya zauna tare da masu gadi, yana jin ɗumin wuta.

  15. Markus 14:55kusan 33 M.

    Manyan firistoci da dukan ’yan Majalisa, suka shiga neman shaidar laifin da za a tabbatar a kan Yesu, domin su kashe shi. Amma ba su sami ko ɗaya ba.

  16. Markus 14:56kusan 33 M.

    Da yawa suka ba da shaidar ƙarya a kansa, amma shaidarsu ba tă zo ɗaya ba.

  17. Markus 14:57kusan 33 M.

    Sai waɗansu suka miƙe tsaye, suka ba da wannan shaida ƙarya a kansa, suka ce,

  18. Markus 14:58kusan 33 M.

    “Mun ji shi ya ce, ‘Zan rushe wannan haikali da mutum ya gina, cikin kwana uku, in sāke gina wani wanda ba ginin mutum ba.’ ”

  19. Markus 14:59kusan 33 M.

    Duk da haka ma, shaidarsu ba tă zo ɗaya ba.

  20. Markus 14:60kusan 33 M.

    Sai babban firist ya tashi a gabansu, ya tambayi Yesu ya ce, “Ba za ka amsa ba? Wane shaida ke nan waɗannan mutane suke kawowa a kanka?”

  21. Markus 14:61kusan 33 M.

    Amma Yesu ya yi shiru, bai kuwa amsa ba. Babban firist ya sāke tambayarsa ya ce, “Kai ne Kiristi, Ɗan Mai Albarka?”

  22. Markus 14:62kusan 33 M.

    Yesu ya ce, “Ni ne. Za ku kuwa ga Ɗan Mutum yana zaune a hannun dama na Mai Iko, yana kuma zuwa a cikin gizagizan sama.”

  23. Markus 14:63kusan 33 M.

    Babban firist ya yage tufafinsa, ya yi ce, “Ina dalilin neman waɗansu shaidu kuma?

  24. Markus 14:64kusan 33 M.

    Kun dai ji saɓon. Me kuka gani?” Duka suka yanke masa hukuncin kisa.

  25. Markus 14:65kusan 33 M.

    Sai waɗansu suka fara tattofa masa miyau, suka rufe masa idanu, suka bubbuge shi da hannuwansu, suka ce, “Yi annabci!” Masu gadin kuma suka ɗauke shi, suka yi masa duka.