circa 6 BC – AD 30
The Life of Jesus
The eternal Son of God enters history: born in Bethlehem, baptized in the Jordan, crucified at Golgotha, raised on the third day.
Ayoyi daga wannan lokacin
- Mattiyu 22:23kusan 33 M.
A ranan nan Sadukiyawa, waɗanda suke cewa babu tashin matattu, suka zo wurinsa da tambaya.
- Mattiyu 22:24kusan 33 M.
Suka ce “Malam, Musa ya faɗa mana cewa in mutum ya mutu ba shi da ’ya’ya, dole ɗan’uwansa yă auri gwauruwar yă kuma haifar wa ɗan’uwan ’ya’ya.
- Mattiyu 22:25kusan 33 M.
A cikinmu an yi ’yan’uwa guda bakwai. Na fari ya yi aure, ya mutu, da yake bai sami ’ya’ya ba, sai ya bar matarsa wa ɗan’uwansa.
- Mattiyu 22:26kusan 33 M.
Haka ya faru da ɗan’uwa na biyu da na uku, har zuwa na bakwai.
- Mattiyu 22:27kusan 33 M.
A ƙarshe, macen ta mutu.
- Mattiyu 22:28kusan 33 M.
To, a tashin matattu, matar wa a cikinsu bakwai ɗin nan za tă zama, da yake dukansu sun aure ta?”
- Mattiyu 22:29kusan 33 M.
Yesu ya amsa ya ce, “Kun ɓata, domin ba ku san Nassi ko ikon Allah ba.
- Mattiyu 22:30kusan 33 M.
Ai, a tashin matattu, mutane ba za su yi aure ko su ba da aure ba; za su zama kamar mala’iku a sama.
- Mattiyu 22:31kusan 33 M.
Amma game da tashi daga matattu na waɗanda suka mutu ba ku karanta abin da Allah ya ce muku ba ne,
- Mattiyu 22:32kusan 33 M.
‘Ni ne Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku da kuma Allah na Yaƙub’? Ai, shi ba Allah na matattu ba ne, shi Allah na masu rai ne.”
- Mattiyu 22:33kusan 33 M.
Da taro suka ji haka, sai suka yi mamakin koyarwarsa.
- Mattiyu 22:34kusan 33 M.
Da jin Yesu ya ƙure Sadukiyawa, sai Farisiyawa suka tattaru.
- Mattiyu 22:35kusan 33 M.
Ɗaya daga cikinsu, wani masanin Doka, ya gwada shi da wannan tambaya.
- Mattiyu 22:36kusan 33 M.
“Malam, wace doka ce mafi girma a cikin dokoki?”
- Mattiyu 22:37kusan 33 M.
Yesu ya amsa ya ce, “ ‘Ka ƙaunaci Ubangiji Allahnka da dukan zuciyarka da dukan ranka da kuma dukan hankalinka.’
- Mattiyu 22:38kusan 33 M.
Wannan, ita ce doka ta fari da kuma mafi girma.
- Mattiyu 22:39kusan 33 M.
Ta biye kuma kamar ta farkon take. ‘Ka ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka.’
- Mattiyu 22:40kusan 33 M.
Dukan Doka da Annabawa suna rataya ne a kan waɗannan dokoki biyu.”
- Mattiyu 22:41kusan 33 M.
Yayinda Farisiyawa suke a tattare wuri ɗaya, sai Yesu ya tambaye su,
- Mattiyu 22:42kusan 33 M.
“Me kuke tsammani game da Kiristi? Ɗan wane ne shi?” Suka amsa suka ce, “Ɗan Dawuda.”
- Mattiyu 22:43kusan 33 M.
Ya ce musu, “To, ta yaya Dawuda ya yi magana ta wurin Ruhu Mai Tsarki, ya kira shi ‘Ubangiji’? Gama ya ce,
- Mattiyu 22:44kusan 33 M.
“ ‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana, sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka.” ’
- Mattiyu 22:45kusan 33 M.
To, in Dawuda ya kira shi ‘Ubangiji,’ yaya zai zama ɗansa?”
- Mattiyu 22:46kusan 33 M.
Ba wanda ya iya tanka masa, daga wannan rana kuwa ba wanda ya sāke yin karambanin yin masa wata tambaya.
- Mattiyu 23:1kusan 33 M.
Sa’an nan Yesu ya ce wa taron mutane da kuma almajiransa,