Tsallake zuwa abun ciki

circa 800–400 BC

The Hebrew Prophets

God speaks through Isaiah, Jeremiah, and the minor prophets—calling Israel to repentance and foretelling the coming Messiah.

3,706 ayoyi · 14 littattafai da aka rufe

Ayoyi daga wannan lokacin

Tace bisa littafi
  1. Hosiya 7:11kusan 780 K.H.

    “Efraim yana kama da kurciya, marar wayo, marar hankali, yanzu yana kira ga Masar, yanzu yana juyewa ga Assuriya.

  2. Hosiya 7:12kusan 780 K.H.

    Sa’ad da suka tafi, zan jefa ragata a kansu; zai janye su ƙasa kamar tsuntsayen sararin sama. Sa’ad da na ji suna tafiya tare, zan kama su.

  3. Hosiya 7:13kusan 780 K.H.

    Kaitonsu, domin sun kauce daga gare ni! Hallaka za tă aukar musu, domin sun tayar mini! Na ƙudura in cece su amma suna faɗar ƙarya a kaina.

  4. Hosiya 7:14kusan 780 K.H.

    Ba sa yin mini kuka da zuciyarsu amma suna ihu a kan gadajensu. Sukan taru wurin ɗaya don hatsi da ruwan inabi amma su juya mini baya.

  5. Hosiya 7:15kusan 780 K.H.

    Na horar da su na kuma ƙarfafa su, amma sun ƙulla mini maƙarƙashiya.

  6. Hosiya 7:16kusan 780 K.H.

    Ba sa juya ga Mafi Ɗaukaka; suna kama da tanƙwararren baka. Za a kashe shugabanninsu da takobi saboda banzan maganganunsu. Saboda wannan za a wulaƙanta su a ƙasar Masar.

  7. Hosiya 8:1kusan 780 K.H.

    “Ka sa kakaki a leɓunanka! Gaggafa tana a bisan gidan Ubangiji domin mutane sun tā da alkawarina suka kuma tayar wa dokata.

  8. Hosiya 8:2kusan 780 K.H.

    Isra’ila ta yi mini kuka, ‘Ya Allahnmu, mun yarda da kai!’

  9. Hosiya 8:3kusan 780 K.H.

    Amma Isra’ila sun ƙi abin da yake mai kyau; abokin gāba zai fafare su.

  10. Hosiya 8:4kusan 780 K.H.

    Suna naɗa sarakuna, ba da izinina ba; sun zaɓa shugabanni ba da yardanta ba. Da azurfa da zinariya sun ƙera gumaka wa kansu wanda zai kai zuwa ga hallakarsu.

  11. Hosiya 8:5kusan 780 K.H.

    Ku zubar da gunkin maraƙinku, ya Samariya! Fushina yana ƙuna a kansu. Sai yaushe za su rabu da gumaka?

  12. Hosiya 8:6kusan 780 K.H.

    Su daga Isra’ila ne! Wannan maraƙi, mai aikin hannu ne ya yi shi; gunki ne ba Allah ba. Za a farfashe shi kucu-kucu, waccan maraƙin Samariya.

  13. Hosiya 8:7kusan 780 K.H.

    “Gama sun shuka iska don haka za su girbe guguwa. Hatsin da yake tsaye ba shi da kai, ba zai yi tsaba ba. Ko da ya yi tsaba ma, baƙi ne za su ci.

  14. Hosiya 8:8kusan 780 K.H.

    An haɗiye Isra’ila; yanzu tana cikin al’ummai kamar abin da ba shi da amfani.

  15. Hosiya 8:9kusan 780 K.H.

    Gama sun haura zuwa Assuriya kamar jakin jejin da yake yawo shi kaɗai. Efraim ya sayar da kansa ga maza.

  16. Hosiya 8:10kusan 780 K.H.

    Ko da yake sun sayar da kansu a cikin al’ummai, yanzu zan tattara su wuri ɗaya. Za su fara lalacewa a ƙarƙashi danniyar babban sarki.

  17. Hosiya 8:11kusan 780 K.H.

    “Ko da yake Efraim ya gina bagadai masu yawa don hadayun zunubi, waɗannan sun zama bagade don yin zunubi.

  18. Hosiya 8:12kusan 780 K.H.

    Na rubuta musu abubuwa masu yawa na dokata, amma suka ɗauke su tamƙar wani baƙon abu ne.

  19. Hosiya 8:13kusan 780 K.H.

    Suna miƙa hadayun da aka ba ni su kuma ci nama, amma Ubangiji ba ya jin daɗinsu. Yanzu zai tuna da muguntarsu yă kuma hukunta zunubansu. Za su koma Masar.

  20. Hosiya 8:14kusan 780 K.H.

    Isra’ila ya manta da Mahaliccinsa ya kuma gina fadodi; Yahuda ya gina katanga a yawancin garuruwansa. Amma zan aiko da wuta a bisa biranensu da zai cinye kagaransu.”

  21. Hosiya 9:1kusan 760 K.H.

    Kada ku yi farin ciki, ya Isra’ila; kada ku yi murna kamar waɗansu al’ummai. Gama kun yi rashin aminci ga Allahnku; kuna son hakkokin karuwa a kowace masussuka.

  22. Hosiya 9:2kusan 760 K.H.

    Masussukai da wuraren matsin inabi ba za su ciyar da mutane ba; sabon ruwan inabi zai kāsa musu.

  23. Hosiya 9:3kusan 760 K.H.

    Ba za su ci gaba da zama a ƙasar Ubangiji ba; Efraim zai koma Masar yă kuma ci abinci marar tsarki a Assuriya.

  24. Hosiya 9:4kusan 760 K.H.

    Ba za su zuba hadayun ruwan inabi ga Ubangiji ba, ba kuwa hadayunsu za su gamshe shi ba. Irin hadayun nan za su zama musu kamar burodin masu makoki; duk wanda ya ci su zai ƙazantu. Wannan abincin zai zama na kansu ne; ba zai zo cikin haikalin Ubangiji ba.

  25. Hosiya 9:5kusan 760 K.H.

    Me za ku yi a ƙayyadaddiyar ranar bukukkuwarku, a ranakun bikin Ubangiji?