God
Ayoyin da suka ambaci God
yadda ruwa yakan zaizaye duwatsu ruwa mai ƙarfi kuma yă kwashe turɓayar ƙasa, haka kake barin mutum ba bege.
Ka sha ƙarfinsa gaba ɗaya, sai ya ɓace, ka sauya yanayinsa ka kuma kore shi.
Amma ka ma rena Allah ka hana a yi addu’a gare shi.
Kana sauraron shawarar Allah? Ko kana gani kai kaɗai ne mai hikima?
Ta’aziyyar Allah ba tă ishe ka ba. Maganarsa mai laushi ba tă ishe ka ba?
har kake fushi da Allah kake kuma faɗar waɗannan maganganu daga bakinka?
In Allah bai nuna amincewa ga tsarkakansa ba, in har sammai ba su da tsarki a idonsa,
domin ya nuna wa Allah yatsa ya rena Allah Maɗaukaki,
ya tasar masa da faɗa da garkuwa mai kauri da kuma ƙarfi.
Allah ya bashe ni ga mugayen mutane, ya jefa ni hannun mugaye.
Dā ina zamana lafiya kome yana tafiya daidai; amma ya ragargaza ni; ya shaƙe ni a wuya; ya murƙushe ni na zama abin barata gare shi;
maharbansa sun kewaye ni. Ba tausayi, ya soke ni a ƙodata har jini ya zuba a ƙasa.
Ya ji mini rauni a kai a kai ya auko mini kamar mai yaƙi.
Shi mai yin roƙo a madadina abokina ne yayinda nake kuka ga Allah;
a madadin mutum ya yi roƙo ga Allah kamar yadda mutum yakan yi roƙo domin abokinsa.
“Ya Allah, ka ba ni abin da ka yi mini alkawari. Wane ne zai kāre ni?
Ka rufe zuciyarsu yadda ba za su iya ganewa ba, saboda haka ba za ka bari su yi nasara ba.
Ba shakka haka wurin zaman mugun mutum yake, haka wurin zaman wanda bai san Allah ba yake.”
sai ku san cewa Allah ya yi mini ba daidai ba ya kewaye ni da ragarsa.
Ya tare mini hanya yadda ba zan iya wucewa ba; ya rufe hanyata da duhu.
Ya yi kaca-kaca da ni har sai da na ƙare; ya tuge begen da nake da shi kamar itace.
Yana jin haushina ya lissafta ni cikin maƙiyansa.
“Ku tausaya mini, abokaina, ku ji tausayina, gama hannun Allah ya sauko a kaina.
Don me kuke fafarata kamar yadda Allah yake yi? Ba ku gaji da yagar fatata ba?
Kuma bayan an hallaka fatata, duk da haka a cikin jiki zan ga Allah.