circa 6 BC – AD 30
The Life of Jesus
The eternal Son of God enters history: born in Bethlehem, baptized in the Jordan, crucified at Golgotha, raised on the third day.
Ayoyi daga wannan lokacin
- Mattiyu 24:38kusan 33 M.
Gama a kwanaki kafin ruwan tsufana, mutane sun yi ta ci, sun kuma yi ta sha, suna aure, suna kuma aurarwa, har zuwa ranar da Nuhu ya shiga jirgi;
- Mattiyu 24:39kusan 33 M.
ba su kuwa san abin da yake faruwa ba sai da ruwan tsufana ya zo ya share su tas. Haka zai zama a dawowar Ɗan Mutum.
- Mattiyu 24:40kusan 33 M.
Maza biyu za su kasance a gona; za a ɗau ɗaya a bar ɗaya.
- Mattiyu 24:41kusan 33 M.
Mata biyu za su kasance suna niƙa; za a ɗau ɗaya a bar ɗaya.
- Mattiyu 24:42kusan 33 M.
“Saboda haka sai ku zauna a faɗake, gama ba ku san a wace rana ce Ubangijinku zai zo ba.
- Mattiyu 24:43kusan 33 M.
Ku dai gane wannan, da maigida ya san ko a wane lokaci ne da dare, ɓarawo zai zo, da sai yă zauna a faɗake yă kuma hana a shiga masa gida.
- Mattiyu 24:44kusan 33 M.
Saboda haka ku ma, sai ku zauna a faɗake, domin Ɗan Mutum zai zo a sa’ar da ba ku za tă ba.
- Mattiyu 24:45kusan 33 M.
“Wane ne bawan nan mai aminci da kuma mai hikima, wanda maigida ya sa yă lura da bayi a cikin gidansa, yă riƙa ba su abinci a daidai lokaci?
- Mattiyu 24:46kusan 33 M.
Zai zama wa bawan nan da kyau in maigidan ya dawo ya same shi yana yin haka.
- Mattiyu 24:47kusan 33 M.
Gaskiya nake gaya muku, zai sa shi yă lura da dukan dukiyarsa.
- Mattiyu 24:48kusan 33 M.
Amma in wannan bawa mugu ne, ya kuma ce a ransa, ‘Maigidana ba zai dawo da wuri ba.’
- Mattiyu 24:49kusan 33 M.
Sa’an nan yă fara dūkan ’yan’uwansa bayi, yana ci yana kuma sha tare da mashaya.
- Mattiyu 24:50kusan 33 M.
Maigidan wannan bawa zai dawo a ranar da bai yi tsammani ba, a sa’ar kuma da bai sani ba.
- Mattiyu 24:51kusan 33 M.
Maigidan zai farfasa masa jiki da bulala, yă kuma ba shi wuri tare da munafukai, inda za a yi kuka da cizon haƙora.
- Mattiyu 25:1kusan 33 M.
“A lokacin mulkin sama zai zama kamar budurwai goma waɗanda suka ɗauki fitilunsu suka fita don su taryi ango.
- Mattiyu 25:2kusan 33 M.
Biyar daga cikinsu wawaye ne, biyar kuma masu hikima.
- Mattiyu 25:3kusan 33 M.
Wawayen sun ɗauki fitilunsu, sai dai ba su riƙe mai ba.
- Mattiyu 25:4kusan 33 M.
Masu hikimar kuwa suka riƙo tulunan mai da fitilunsu.
- Mattiyu 25:5kusan 33 M.
Ango ya yi jinkirin zuwa, sai duk suka shiga gyangyaɗi har barci ya kwashe su.
- Mattiyu 25:6kusan 33 M.
“Can tsakar dare, sai aka ji kira, ana cewa, ‘Ga ango nan! Ku fito, ku tarye shi!’
- Mattiyu 25:7kusan 33 M.
“Sai dukan budurwan nan suka farka suka kuna fitilunsu.
- Mattiyu 25:8kusan 33 M.
Sai wawayen suka ce wa masu hikimar, ‘Ku ɗan sassam mana manku; fitilunmu suna mutuwa.’
- Mattiyu 25:9kusan 33 M.
“Su kuwa suka amsa, suka ce, ‘A’a, wataƙila ba zai ishe mu da ku ba. Gara ku je wurin masu sayarwa ku sayo.’
- Mattiyu 25:10kusan 33 M.
“Amma yayinda suke kan tafiya garin sayen mai, sai ango ya iso. Budurwai da suke a shirye, suka shiga wajen bikin auren tare da shi. Aka kuma kulle ƙofa.
- Mattiyu 25:11kusan 33 M.
“An jima can, sai ga sauran sun iso. Suka ce, ‘Ranka yă daɗe! Ranka yă daɗe! Ka buɗe mana ƙofa!’