Tsallake zuwa abun ciki

circa 1380–1050 BC

The Judges & Ruth

Israel cycles through rebellion, oppression, and rescue under charismatic leaders—culminating in Ruth's faithful love story.

703 ayoyi · 2 littattafai da aka rufe

Ayoyi daga wannan lokacin

Tace bisa littafi
  1. Mahukunta 20:6kusan 1406 K.H.

    Na ɗauki ƙwarƙwarata na yayyanka gunduwa-gunduwa na aika da shi ga kowane yankin gādon Isra’ila, domin sun aikata mugu abu da abin kunya a Isra’ila.

  2. Mahukunta 20:7kusan 1406 K.H.

    To, dukanku Isra’ilawa, sai ku yi magana ku kuma yanke hukuncinku.”

  3. Mahukunta 20:8kusan 1406 K.H.

    Dukan mutane suka tashi kamar mutum ɗaya, suna cewa “Ba waninmu da zai tafi gida. Sam, babu ko ɗayanmu da zai koma gidansa.

  4. Mahukunta 20:9kusan 1406 K.H.

    Amma yanzu ga abin da za mu yi wa Gibeya. Za mu haura mu fāɗa yadda ƙuri’a ta nunar.

  5. Mahukunta 20:10kusan 1406 K.H.

    Za mu ɗauko mutum goma a kowane mutum ɗari daga dukan kabilan Isra’ila, da ɗari a dubu, da kuma dubu a dubu goma, domin a tanada wa mayaƙan. Sa’an nan, sa’ad da mayaƙan suka iso Geba a Benyamin, za su yi da su daidai bisa ga muguntar da suka yi a Isra’ila.”

  6. Mahukunta 20:11kusan 1406 K.H.

    Saboda haka dukan mutane Isra’ilawa suka taru suka kuma haɗu kamar mutum guda don su fāɗa wa birnin da yaƙi.

  7. Mahukunta 20:12kusan 1406 K.H.

    Kabilan Isra’ila suka aika jakadu a ko’ina a cikin kabilar Benyamin cewa, “Wace irin mugunta ce wannan da kuka aikata?

  8. Mahukunta 20:13kusan 1406 K.H.

    Yanzu fa sai ku fitar da waɗannan ’yan iskan da suka aikata wannan abu na Gibeya don mu kashe su mu kawar da mugunta daga Isra’ila!” Amma mutanen Benyamin ba su saurari ’yan’uwansu Isra’ilawa ba.

  9. Mahukunta 20:14kusan 1406 K.H.

    Daga biranensu suka tattaru a Gibeya don su yaƙi Isra’ilawa.

  10. Mahukunta 20:15kusan 1406 K.H.

    Nan da nan mutanen Benyamin suka tattara mayaƙa dubu ashirin da shida masu takuba daga biranensu, ban da mayaƙa ɗari bakwai da aka zaɓa daga mazauna a Gibeya.

  11. Mahukunta 20:16kusan 1406 K.H.

    Cikin dukan mayaƙan nan akwai zaɓaɓɓu mutane ɗari bakwai waɗanda su bahagwai ne, kowanne yana iya harbin gashin guda na kai da majajjawa ba kuskure.

  12. Mahukunta 20:17kusan 1406 K.H.

    Isra’ila kuwa, ban da Benyamin, sun tara mayaƙa masu takobi dubu ɗari huɗu, dukansu gwanayen yaƙi ne.

  13. Mahukunta 20:18kusan 1406 K.H.

    Sai Isra’ilawa suka haura zuwa Betel suka nemi nufin Allah, suka ce, “Wane ne a cikinmu zai fara fāɗa wa mutanen Benyamin?” Ubangiji ya ce, “Yahuda ce za tă fara.”

  14. Mahukunta 20:19kusan 1406 K.H.

    Kashegari sai Isra’ilawa suka tashi suka kafa sansani kusa da Gibeya.

  15. Mahukunta 20:20kusan 1406 K.H.

    Mutanen Isra’ila suka fita yaƙi da mutane Benyamin suka kuma ja dāgār yaƙi a Gibeya.

  16. Mahukunta 20:21kusan 1406 K.H.

    Mutanen Benyamin suka fito daga Gibeya suka kashe mutum dubu ashirin da biyu na Isra’ilawa a dāgār yaƙi a ranar.

  17. Mahukunta 20:22kusan 1406 K.H.

    Amma mutanen Isra’ila suka ƙarfafa juna, suka sāke koma inda suka ja dāgā a rana ta farko.

  18. Mahukunta 20:23kusan 1406 K.H.

    Isra’ilawa suka haura suka yi kuka a gaban Ubangiji, har yamma, suka nemi nufin Ubangiji. Suka ce, “Mu sāke koma yaƙi da mutanen Benyamin, ’yan’uwanmu?” Ubangiji ya ce, “Ku haura ku fāɗa musu.”

  19. Mahukunta 20:24kusan 1406 K.H.

    Sai Isra’ilawa suka matsa kusa da Benyamin a rana ta biyu.

  20. Mahukunta 20:25kusan 1406 K.H.

    A wannan lokaci, da mutanen Benyamin suka fito daga Gibeya don su yaƙe su, sai suka sāke kashe Isra’ilawa dubu goma sha takwas, dukansu ɗauke da takuba.

  21. Mahukunta 20:26kusan 1406 K.H.

    Sa’an nan Isra’ilawa, dukan mutane, suka haura zuwa Betel, a can suka zauna suna kuka a gaban Ubangiji. Suka yi azumi a wannan rana har yamma suka miƙa hadayun ƙonawa da hadayun salama ga Ubangiji.

  22. Mahukunta 20:27kusan 1406 K.H.

    Isra’ilawa suka nemi nufin Ubangiji (A kwanakin nan akwatin alkawarin Allah yana can,

  23. Mahukunta 20:28kusan 1406 K.H.

    Finehas ɗan Eleyazar, ɗan Haruna, kuwa yana hidima a gabansa.) Suka ce, “Mu sāke haura mu yi yaƙi da mutanen Benyamin ’yan’uwanmu, ko a’a?” Ubangiji ya ce, “Ku je, gama gobe zan ba da su a hannuwanku.”

  24. Mahukunta 20:29kusan 1406 K.H.

    Sa’an nan Isra’ila ta yi kwanto kewaya da Gibeya.

  25. Mahukunta 20:30kusan 1406 K.H.

    Suka haura su kara da mutanen Benyamin a rana ta uku suka ja dāgā a Gibeya kamar dā.