Tsallake zuwa abun ciki

Ayoyin Littafi Mai Tsarki game da Young Men

347 ayoyi · 1 fanni

Mahimman ayoyin Littafi Mai Tsarki

Tace bisa littafi
  1. Amma hanyar mugaye kamar zurfin duhu ne; ba sa sanin abin da ya sa suke tuntuɓe.

  2. Ɗana, ka kula da abin da nake faɗa, ka saurara sosai ga kalmomina.

  3. Kada ka bari su rabu da kai, ka kiyaye su a cikin zuciyarka;

  4. gama rai ne ga waɗanda suke nemansu da kuma lafiya ga dukan jikin mutum.

  5. Fiye da kome duka, ka tsare zuciyarka, gama maɓulɓulan ruwan rijiyar rai ne.

  6. Ka kau da muguwar magana daga bakinka; ka yi nesa da magana marar kyau daga leɓunanka.

  7. Bari idanunka su dubi gaba sosai, ka kafa idanunka kai tsaye a gabanka.

  8. Ka san inda ƙafafunka suke takawa ka bi hanyoyin da suke daram kawai.

  9. Kada ka kauce dama ko hagu; ka kiyaye ƙafarka daga mugunta.

  10. Ɗana, ka mai da hankali ga hikimata ka saurara da kyau ga kalmomin basirata,

  11. don ka ci gaba da yin kome daidai leɓunanka za su adana sani.

  12. Gama leɓunan mazinaciya na ɗigan zuma, maganarta tana da sulɓi fiye da mai;

  13. amma a ƙarshe tana da ɗaci kamar tafashiya, mai ci kamar takobi mai kaifi biyu.

  14. Ƙafafunta na kaiwa ga mutuwa; sawunta na jagora kai tsaye zuwa kabari.

  15. Ba ta wani tunanin rayuwa; hanyoyinta karkatacce ne, amma ba tă sani ba.

  16. Yanzu fa, ’ya’yana, ku saurare ni; kada ku juye daga abin da nake faɗa.

  17. Ku yi nesa da hanyarta, kana ku je kusa da ƙofar gidanta,

  18. don kada ku ba da ƙarfi mafi kyau ga waɗansu da kuma shekarunku ga wani marar imani,

  19. don kada baƙi su yi biki a kan dukiyarku wahalarku ta azurta gidan wani mutum dabam.

  20. A ƙarshen rayuwarku za ku yi ta nishi, sa’ad da namanku da jikinku suka zagwanye.

  21. Za ku ce, “Me ya sa na ƙi horo! Me ya sa zuciyata ta ƙi gyara!

  22. Ban yi biyayya da malamaina ba ko in saurari masu koyar da ni.

  23. Na zo gab da hallaka gaba ɗaya a tsakiyar dukan taron.”

  24. Ku sha ruwa daga tankinku, ruwa mai gudu daga rijiyarku.

  25. In maɓulɓulanku suka cika suna malala har waje, rafuffukan ruwanku a dandalin jama’a?